• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yobe Ta Arewa: Yadda Take Kayawa A Yakin Neman Zaben Bashir Machina Bayan Kada Ahmad Lawan

by Muhammad Maitela
3 years ago
Machina

Duk da kiki-kaka da zaman tankiya da ake ci gaba da fuskanta tsakanin magoya bayan Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Lawan da bangaren Hon. Bashir Machina, kan takarar Sanatan Yobe ta Arewa a karkashin jam’iyyar APC, hakan ba ta hana gudanar da gangamin yakin neman zaben ba.

Muhammed Dauda Sa’id (Gaskanta) shi ne Ko’odinatan yakin neman zaben dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa, Hon. Bashir Machina, inda ya bayyana wa wakilinmu a jihar Yobe cewa, duk da rashin fahimtar da wasu daga cikin magoya bayan Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad Lawan suka yi wa al’amarin, amma hakan bai hana yakin neman zaben samun gagarumar tarba daga al’ummar yankin ba.

  • Ban Taba Nadamar Kai Kara Kotu Kan Takarata Ba – Machina

Ya ce, a tarukan da suka gudanar a kananan hukumomin Nguru, Karasuwa, Machina da Gashuwa, ya gudana cikin nasara tare da nuna goyon bayan dubun-dubatar jama’a. Ya ce wannan alamu ne da suka nuna al’ummar yankin suna cike da shaukin samun canjin sabon hannu don ya jagoranci Yobe ta Arewa zuwa ga samun ci gaba mai dorewa, bayan zaben 2023.

“Kuma a matsayina na Ko’odinatan yakin neman zaben sa, abin alfahari ne gareni bisa yawan jama’ar da suka fito maza da mata, yara da manya- jama’a ne ke tururuwa daga Ofishin Yan-sanda na bakin garin Gashuwa zuwa kofar Fadar Mai Bade; tazarar kilomita daya da digo biyar, sai da ya kwashe awanni biyu da minti 5 kafin ya isa Kofar Fada.

Saboda yadda jama’a ke daukin samun sabon canji.”
Hon. Gaskanta ya kara da cewa, wannan karbuwa da Hon. Bashir Machina yake samu alamun nasara ne, saboda dukanmu ya’yan jam’iyyar APC ne, kuma mutane ba a shirye suke su bar jam’iyyar ba, masu da’a da biyayya ne ga jam’iyyar APC. “Babu yadda za a yi irin wannan sabanin da aka samu ya hana cikakken dan jam’iyyar yaki zabar mutumin da jam’iyyar ta tsayar ba.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Sannan wannan rigimar bata yi tsamin irin wadda ta faru tsakanin marigayi Gwamna Mamman B. Ali da marigayi Sanata Usman Al-Bashir ba, saboda shi Sanata Ahmed Lawan bai yi takarar Sanatan Yobe ta Arewa ba, face kawai shugaban jam’iyyar APC na kasa ne yake neman ya kwace kujerar ya bashi.”

Ya kara da cewa, “Sannan kuma shi Shugaban jam’iyyar APC na kasa bai fito ta hanyar lalama ba, saboda mu ‘ya’ya ne, kanne, kuma iyaye a wata fuskar, kuma da ace an bukaci zama da Hon. Bashir Machina da mu magoya bayan sa, a nemi taimakonmu a lokacin da Sanata Ahmed Lawan ya fadi zaben fidda-gwani na Shugaban kasa, a nemi alfarmar a bar masa takarar Sanatan Yobe ta Arewa, wannan daidai ce. Amma ba ta nuna karfin shugabancin jam’iyya ba.” Ya nanata.

“Kuma matakin da Hon. Bashir Machina ya dauka na zuwa kotu daidai ne, saboda ba a nemeshi ta sulhu ba, sai ake neman ayi masa ‘ko da tsaiya-tsiya, ko da karfin tsiya’ ka ga dole ya garzaya inda za a kwata masa hakkinsa; inda mu mabiyansa muka goya masa baya har Allah ya bashi nasara a kotu karon farko da na biyu. Ko in Sha Allah yadda jama’a suka yi maraba dashi haka zasu jefa masa kuri’a cikin nasara.”

Ko’odinatan ya kara da cewa, kwamitin yakin neman zaben Hon. Bashir Machina suna kai-komo wajen lallashin magoya bayan Shugaban Majalisar Dattawan, suna binsu gida-gida tare da basu hakuri, ya ce, “Shima Sanata Ahmed Lawan zamu nada kwamiti mu sameshi har gida mu bashi hakuri.

Saboda dukanmu ya’yan jam’iyyar APC ne kuma a karkashin Limamin Sulhu, Hon. Mai Mala Buni, wanda kowa ya san matsayin sa na sulhunta ya’yan jam’iyyar APC a matakin kasa ba a Yobe kadai ba.”

A hannu guda kuma, Muhammed Dauda Sa’id ya kara da cewa, babban kuskure ne wani ya zargi Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni kan goyon bayan wani bangare ko nuna bambanci tsakani.

Ya ce rashin adalci ne a zargi Gwamna saboda shi uban kowa ne kuma babu wata hujja ko shaida a Kan hakan, face kawai zance ne maras tushe da makama. Ya ce, “Kowa ya san wanda ya haddasa mana wannan fitina ta cikin gida, ba kowa bane face Shugaban jam’iyyar APC na kasa.”

A karshe ya bayyana cewa, “Muna kira ga daukwacin al’ummar wannan yanki da jihar Yobe baki daya, kowa ya hakura a hada kai ayi abu guda kuma mu fuskanci ci gaban yankin mu da jiharmu dama kasa baki daya. Kuma muna kira ga matasanmu don Allah ayi hakuri a mutunta juna kuma a guji bangar siyasa a mutunta juna.

Sannan bama goyon bayan duk wani aiki ko kamalan cin zarafi da bayyana kiyayya ga junanumu, muna ba kowa hakuri azo ayi aiki tare.” Ya nanata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Siyasa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Next Post
Gurbacewar Tarbiyyar Matasa:  Wasika Zuwa Ga Iyaye!

Gurbacewar Tarbiyyar Matasa: Wasika Zuwa Ga Iyaye!

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.