• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
Arewa

Wasu jiga-jigan kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF) sun yi wani sabon yunkuri na mara baya ga dan takarar shugaban kasa daga arewa a zaben 2027, wanda suke ganin cewa dan yankin arewa ne kadai zai iya kishin magance tarin matsaloli da yankin ke fuskanta a halin yanzu.

Wannan matsayi ya fito ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun, Sakataren Yada Labarai na ACF na kasa, Farfesa Tukur Muhammad Baba, kuma ya raba wa manema labarai bayan taron majalisar zartaswa ta kasa da kungiyar ta gudanar a Kaduna.

  • Bayani Kan Zubewar Gashi
  • Zulum Ya Yi Kira Ga Sanatocin Arewa Da Su Ƙi Yarda Da Sabon Tsarin Haraji

Sanarwar ta ce, taron majalisar zartarwa ta ACF, ya yi bitar abubuwan da ke faruwa a arewa da ma kasa baki daya.

“An gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa na kungiyar ACF a hedikwatarta da ke Kaduna a ranar Laraba 20 ga Satumba, 2024. Wakilai a taron sun fito ne daga jihohin arewa da kuma mambobin kungiyar da ke zaune a kasashen waje, wanda shugaban majalisar zartarwa ta kungiyar, Mamman Mike Osuman, ya jagoranta. Taron ya duba ayyukan ACF tun daga taron na Mayun 2024.”

“A jawabinsa na bude taron, shugaban ya yi maraba da mambobin kungiyar tare da nuna gamsuwa da sake farfado da harkokin kungiyar ACF a matsayinta na babbar kungiyar da ke kare muradu, al’adu da zamantakewar al’umma, wadda ke kokarin hada kan al’ummar arewa daban-daban da mabanbantan ra’ayi da manufa daya, tare da hadin kai wajen ganin an cimma nasarar gudanar muradun al’ummar arewa a cikin Nijeriya. Shugaban ya ja kunnen ‘yan kungiyar da su ci gaba da mai da hankali, musamman kan muradun arewa da kuma manufofin ACF, domin akwai abubuwa da yawa da ya kamata a yi kuma lokaci ya kure.

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

“Shugaban ya umurci sauran shugabannin kungiyar na rassa daban-daban su kasance cikin manufa guda, tare da kawar da bambance-bambancen addini da na kabilanci, amma su yi kokarin tabbatar da dangantaka mai kyau da gwamnonin jihohi.

“Daga wurin taron, an tattauna batun yanayin yadda al’ummar arewa da ma Nijeriya suke fuskar, inda aka mayar da hankali kan tattalin arziki, yanayin da ake ciki, tsaro, kalubalen zamantakewa, zaman lafiya, da ci gaban siyasa.

“Taron ya yi nuni da cewa, al’ummar arewa na ci gaba da fuskantar tabarbarewar al’amura, kasancewar a halin yanzu yankin ya fi samun koma-bayan tattalin arziki idan aka kwatanta da sauran sassan Nijeriya.

“Yankin na fama da matsananciyar rashin wadataccen abinci, kuma matasansa ba su da ilimi da sanin makamar aiki. Yanzu ne lokacin yin tunani. Duk da irin halin da Arewa ke ciki na fuskantar kalubalen tattalin arziki, manufofin gwamnatin tarayya na ci gaba da dagula al’amura, tare da nuna rashin sanin ya kamata dangane da halin da al’ummar arewa ke ciki.

“Kira ga gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ta sake duba al’amura da sake tsara alkiblar manufofinta na tattalin arziki ta yadda za su dace da bukatun al’ummar arewa.

“Muna kira da babbar murya ga gwamnonin jihohin arewa da su rungumi tsarin aiwatar da manufofi masu karfi, tare da hadin kai, musamman ta fuskar tsaro, ilimi, koyon sana’o’i, noma, da harkokin kiwon lafiya.

“Rashin wadatar wutar lantarki zai ci gaba da kawo cikas ga kokarin da ake na magance fatara, rashin aikin yi, da rashin ci gaba a yankin. Wadannan dole ne a magance su cikin gaggawa.”

Kungiyar ta ce wannan mataki na da nufin ceto yankin arewa daga gazawar shugabanci da matsalolin da ake fuskanta.

ACF ta nuna goyon bayanta ga kungiyar ‘League of Northern Democrats’ (LND), wata sabuwar kungiya da ta dukufa wajen magance matsalolin yankin arewa, ciki har da rashin aikin yi, ilimi, da tasirin siyasa.

Kawunan dattawan arewa dai ya rabu a zaben 2023, duk da dai ACF da NEF sun bayyana cewa bakin su a hade yake, amma kowa ya nuna cewa ba haka ba ne.

Ta ina kangiyar ACF za ta fara? Sabon abu ne za ta zo da shi ko kuma ta yaya lamarin zai tabbata?

Tun da na farko, akwai kalubalen hadin kai a arewa, saboda yanayin yadda aka farraka kabilu, maimakon kishin arewa, wanda a baya babu maganar kai dan arewa ta kudu ne ko ta tsaki. Amma yanzu da yawan kabilu a arewa idan a ce musu su ‘yan arewa, sai su ce su ba ‘yan arewa ba ne.

Wannan yunkuri abu ne mai kyau kamar yadda wasu yankuna suke yi. Kungiyar Yarbawa an ga yadda take magana da murya daya. Haka nan kungiyar dattawan Ibo suma suna da wannan. Amma yanzu a arewa babu kungiya guda daya tilo, wanda ko a kungiyar dattawan arewa sun rabu kashi buyu, haka kuma kungiyar Fulani ta Meyatt Allah ta rabu kashi-kashi.

Masana suna ganin cewa tana ita za a fara irin wannan yunkurin a yankin arewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu
Labarai

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe
Labarai

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Next Post
ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.