• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Labarai, Siyasa
0
Yunkurin ACF Na Mara Wa Dan Takarar Arewa Baya A 2027 : Ta Ina Za A Fara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu jiga-jigan kungiyar tuntuba ta Arewa (ACF) sun yi wani sabon yunkuri na mara baya ga dan takarar shugaban kasa daga arewa a zaben 2027, wanda suke ganin cewa dan yankin arewa ne kadai zai iya kishin magance tarin matsaloli da yankin ke fuskanta a halin yanzu.

Wannan matsayi ya fito ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun, Sakataren Yada Labarai na ACF na kasa, Farfesa Tukur Muhammad Baba, kuma ya raba wa manema labarai bayan taron majalisar zartaswa ta kasa da kungiyar ta gudanar a Kaduna.

  • Bayani Kan Zubewar Gashi
  • Zulum Ya Yi Kira Ga Sanatocin Arewa Da Su Ƙi Yarda Da Sabon Tsarin Haraji

Sanarwar ta ce, taron majalisar zartarwa ta ACF, ya yi bitar abubuwan da ke faruwa a arewa da ma kasa baki daya.

“An gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa na kungiyar ACF a hedikwatarta da ke Kaduna a ranar Laraba 20 ga Satumba, 2024. Wakilai a taron sun fito ne daga jihohin arewa da kuma mambobin kungiyar da ke zaune a kasashen waje, wanda shugaban majalisar zartarwa ta kungiyar, Mamman Mike Osuman, ya jagoranta. Taron ya duba ayyukan ACF tun daga taron na Mayun 2024.”

“A jawabinsa na bude taron, shugaban ya yi maraba da mambobin kungiyar tare da nuna gamsuwa da sake farfado da harkokin kungiyar ACF a matsayinta na babbar kungiyar da ke kare muradu, al’adu da zamantakewar al’umma, wadda ke kokarin hada kan al’ummar arewa daban-daban da mabanbantan ra’ayi da manufa daya, tare da hadin kai wajen ganin an cimma nasarar gudanar muradun al’ummar arewa a cikin Nijeriya. Shugaban ya ja kunnen ‘yan kungiyar da su ci gaba da mai da hankali, musamman kan muradun arewa da kuma manufofin ACF, domin akwai abubuwa da yawa da ya kamata a yi kuma lokaci ya kure.

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

“Shugaban ya umurci sauran shugabannin kungiyar na rassa daban-daban su kasance cikin manufa guda, tare da kawar da bambance-bambancen addini da na kabilanci, amma su yi kokarin tabbatar da dangantaka mai kyau da gwamnonin jihohi.

“Daga wurin taron, an tattauna batun yanayin yadda al’ummar arewa da ma Nijeriya suke fuskar, inda aka mayar da hankali kan tattalin arziki, yanayin da ake ciki, tsaro, kalubalen zamantakewa, zaman lafiya, da ci gaban siyasa.

“Taron ya yi nuni da cewa, al’ummar arewa na ci gaba da fuskantar tabarbarewar al’amura, kasancewar a halin yanzu yankin ya fi samun koma-bayan tattalin arziki idan aka kwatanta da sauran sassan Nijeriya.

“Yankin na fama da matsananciyar rashin wadataccen abinci, kuma matasansa ba su da ilimi da sanin makamar aiki. Yanzu ne lokacin yin tunani. Duk da irin halin da Arewa ke ciki na fuskantar kalubalen tattalin arziki, manufofin gwamnatin tarayya na ci gaba da dagula al’amura, tare da nuna rashin sanin ya kamata dangane da halin da al’ummar arewa ke ciki.

“Kira ga gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ta sake duba al’amura da sake tsara alkiblar manufofinta na tattalin arziki ta yadda za su dace da bukatun al’ummar arewa.

“Muna kira da babbar murya ga gwamnonin jihohin arewa da su rungumi tsarin aiwatar da manufofi masu karfi, tare da hadin kai, musamman ta fuskar tsaro, ilimi, koyon sana’o’i, noma, da harkokin kiwon lafiya.

“Rashin wadatar wutar lantarki zai ci gaba da kawo cikas ga kokarin da ake na magance fatara, rashin aikin yi, da rashin ci gaba a yankin. Wadannan dole ne a magance su cikin gaggawa.”

Kungiyar ta ce wannan mataki na da nufin ceto yankin arewa daga gazawar shugabanci da matsalolin da ake fuskanta.

ACF ta nuna goyon bayanta ga kungiyar ‘League of Northern Democrats’ (LND), wata sabuwar kungiya da ta dukufa wajen magance matsalolin yankin arewa, ciki har da rashin aikin yi, ilimi, da tasirin siyasa.

Kawunan dattawan arewa dai ya rabu a zaben 2023, duk da dai ACF da NEF sun bayyana cewa bakin su a hade yake, amma kowa ya nuna cewa ba haka ba ne.

Ta ina kangiyar ACF za ta fara? Sabon abu ne za ta zo da shi ko kuma ta yaya lamarin zai tabbata?

Tun da na farko, akwai kalubalen hadin kai a arewa, saboda yanayin yadda aka farraka kabilu, maimakon kishin arewa, wanda a baya babu maganar kai dan arewa ta kudu ne ko ta tsaki. Amma yanzu da yawan kabilu a arewa idan a ce musu su ‘yan arewa, sai su ce su ba ‘yan arewa ba ne.

Wannan yunkuri abu ne mai kyau kamar yadda wasu yankuna suke yi. Kungiyar Yarbawa an ga yadda take magana da murya daya. Haka nan kungiyar dattawan Ibo suma suna da wannan. Amma yanzu a arewa babu kungiya guda daya tilo, wanda ko a kungiyar dattawan arewa sun rabu kashi buyu, haka kuma kungiyar Fulani ta Meyatt Allah ta rabu kashi-kashi.

Masana suna ganin cewa tana ita za a fara irin wannan yunkurin a yankin arewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Siyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Next Post

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

9 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

12 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

14 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

16 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Next Post
ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.