ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ICPC Na Bin Diddigin Ayyukan Mazabu Na Naira Biliyan 21 A Kaduna

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kaduna

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta ICPC ta fara bin diddigin ayyukan mazabu na naira biliyan 21 a fadin Jihar Kaduna.

Hukumar ta ce matakin na daga cikin kokarinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen gudanar da ayyuka ga jama’a.

  • An Gano Buhunan Shinkafar Tallafi 16,800 Mai Nauyin Kilo 50 Da Aka Sauyawa Buhu A Kano
  • Yara 160,000 Ke Rayuwa Da Cutar Ƙanjamau A Nijeriya —NACA

Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna, babban sufeto na ICPC, Haruna Aminu, wanda ya wakilci sashen bin diddigi na mazaba da zartarwa a karkashin jagorancin shugaban ICPC, Dakta Musa Adamu Aliyu, ya ce hukumar na bibiyar ayyuka 60 a fadin Jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT

“Mun zo nan ne domin bin diddigin ayyuka kusan 60 a fadin Jihar Kaduna da adadin kudinsu ya kai naira biliyan 21. Mun fara ne a ranar Laraba a yankin Kafanchan, inda muka binciki akalla ayyuka 21. Yanzu haka muna babban garin Kaduna, Unguwar Kabala, muna mai da hankali kan ayyuka irin su fitulun titi mai amfani da hasken rana da aka saka a fadin garin.

“Gaba daya dai, a kan aikin hasken rana, mun ga matakin da ake kai na aiwatarwa, sannan kuma daga dayan kusurwar, mun sami damar gano wasu ayyukan. Wannan aiki ne da ya taba rayuwar mutane,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ya kuma ce hukumar za ta ga yadda za ta tura dan kwangilar ya kammala aikin, inda ya nuna cewa babu wani dan kwangila da za a tsallake saboda ba zai yiwu ba su karbi kudin gwamnati su tafi ba tare da kammala ayyuka ba.

Ya ce zamanin watsi da ayyuka ya wuce domin an ba su dukkan umarni da goyon baya don tunkarar duk wadanda suka kasa kamala ayyukansu a kan lokaci.

Aminu ya bayyana cewa jinkirin da aka samu wajen kammala wasu ayyuka, musamman fitilun titi masu amfani da hasken rana ya kawo cikas ga tasirinsa ga al’umma.

“Wadannan ayyuka na da muhimmanci wajen inganta rayuwa a Jihar Kaduna. Idan aka kammala a shekarar da ta gabata kamar yadda aka tsara, da a yanzu za su kawo gagarumin sauyi,” in ji shi.

Ya ce mataki na gaba na wannan yunkuri zai kunshi dakushe ‘yan kwangilar da suka kasa gudanar da ayyukansu, da tabbatar da cewa ‘yan kasa sun samu ribar dimokuradiyya.

Kaduna
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Next Post
Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

Tashar Wutar Kainji Da Jebba Sun Yi Asarar Naira Biliyan 30 Sakamakon Katsewar Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.