• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen 2023: NIS Ta Ƙwace Katin Zaɓe Da Na Ɗan Ƙasa 6,216 Daga Baƙin Waje

Mun Ƙara Shan Ɗamara Tare Da Sanya Ido - CGI Isah Jere

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Zaɓen 2023: NIS Ta Ƙwace Katin Zaɓe Da Na Ɗan Ƙasa 6,216 Daga Baƙin Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunƙuri na tabbatar da baƙi daga maƙwabta ba su yi katsalandan a zaɓen Nijeriya na 2023 ba, Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) ta ƙwace katunan zaɓe da katin ɗan ƙasa daga hannun baƙin waje guda 6,216 a iyakokin ƙasar guda 21.

Shugaban hukumar ta NIS, CGI Isa Idris Jere ya nuna wa manema labarai katin ɗan ƙasa 3,823 da katin zaɓe 2,393 wanda aka ƙwace daga hannun baki a wasu iyakokin ƙasar nan da suka haɗa da jihohin Nasarawa, Kebbi, Sakwato, Adamawa, Akwa Ibom, Kogi, Yobe, Kwara, Taraba, Filato, Legas, Ogun, Oyo, Zamfara, Jigawa, Edo, Bauchi da Neja da sauran guda uku.

Zabe
Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba lokacin da hukumar ta yi ganawar gaggawa da manyan jami’anta da suka haɗa da kodinetoci na rassa da kwamandojinta da ke faɗin Nijeriya a shalkwatanr hukumar a Abuja, kan shirye-shiryen da hukumar za ta gudanar lokacin zaɓe.

CGI Jere ya ja kunnen jami’ansa kan su ɗauki ranakun 25 ga watan Fabrairu da 11 ga watan Maris na 2023, a matsayin wata dama ta nuna ƙwarewarsu wajen kula da iyakokin ƙasa da tattara bayanan sirri.

Ya gargaɗe su da cewa duk wani jami’i da aka samu yana haɗa kai domin cin amanar ƙasa za a ɗauke shi a matsayin mai zagon ƙasa kuma zai fuskanci fushin hukumar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Zabe
Shugaban hukumar ya yi gargaɗin cewa tsauraran matakai na jiran duk wani baƙo da ya yi yunƙurin shiga harkokin zaɓen ƙasar nan. Inda ya yi ƙarin hasken cewa, tun daga lokacin da aka kama waɗannan baki an mayar da su ƙasashensu ne bisa bin dokar Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) kan ‘yancin tafiye-tafiye.

A cewarsa, dokar zaɓe ta 2022 da kuma kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 da aka yi wa kwaskwarima sun ɗora nauyi a kan masu ruwa da tsaki a harkokin zaɓe, musamman ma hukumar NIS, “wannan ne ya sa muka yanke shawarar ɗora wa kwanturololinmu alhakin duk wata gazawa da jami’ansu suka nuna.”
CGI Jere ya nanata aniyar gwamnati ta tabbatar da sahihin zaɓe na gaskiya da adalci, sannan ya buƙaci manyan jami’an hukumar da su ƙara ƙaimi a dukkan iyakokin ƙasar nan lokacin gudanar da ayyukansu domin tabbatar da samun nasarar zaɓe.

Zaɓe
Ya jaddada wajibcin nuna ɗa’a daga jami’ai da kuma jajircewa wajen ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.
Ya ce, “A matsayinmu na jami’an gwamnati, an haramta mana nuna ɓangaranci a lokacin zaɓe da kuma bayan zaɓe. Domin haka, hukumar tana amfani da wannan damar wajen wayar da kan dukkan ma’aikata ta hannun kwanturololin bisa buƙatar su ci gaba da kasancewa ‘yan babu ruwanmu gabanin zaɓe da lokacin zaɓe da kuma bayan zaɓe.

“Idan ba mu manta ba cewa rattaba hannu kan dokar zaɓe ta 2022 da shugaban ƙasa ya yi a bara, ya sa hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta fitar da jadawalin lokacin zaɓe, inda ta tsayar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya a ranar 25 ga Fabrairu, 2023, sannan zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun jiha zai biyo baya a ranar 11 ga Maris, 2023.

“Dukkanmu muna sane da irin muhimmancin da gwamnatin tarayya ta bai wa Zaɓen 2023 wanda zai kawo ƙarshen mulkin shekaru 8 na gwamnatin da ke ci yanzu, sannan kuma ƙara cika shekaru 24 da dawowar mulkin dimokuraɗiyya a ƙasarmu mai albarka,” in ji shugaban NIS.

Ya kuma yi gargaɗin cewa duk wani mai zagon ƙasa ko rashin ɗa’a gabanin zaɓe da da lokacin zaɓen da kuma bayan zaɓen zai fuskanci hukunci mai tsanani.

Ya umurci manyan jami’an shige da ficen na ƙananan hukumomi 774 da ke faɗin ƙasar nan da su zurfafa sa ido cikin sirri kan hulɗa da bakin ‘yan ƙasashen waje a dukkan yankunansu domin tabbatar da cewa babu wani baƙo da ya shiga cikin harkokin zaɓen Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sauyin Kudi: Almajirai Sun Yi Kukan Yunwa Kan Karancin Samun Kudi A Hannu

Next Post

Kasar Sin Na Samar Da Agajin Jin Kai Ga Wadanda Girgizar Kasa Ta Shafa A Syria

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

8 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

9 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

10 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

12 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

14 hours ago
Next Post
Kasar Sin Na Samar Da Agajin Jin Kai Ga Wadanda Girgizar Kasa Ta Shafa A Syria

Kasar Sin Na Samar Da Agajin Jin Kai Ga Wadanda Girgizar Kasa Ta Shafa A Syria

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.