ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen 2023: NIS Ta Ƙwace Katin Zaɓe Da Na Ɗan Ƙasa 6,216 Daga Baƙin Waje

Mun Ƙara Shan Ɗamara Tare Da Sanya Ido - CGI Isah Jere

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Zaɓe

A wani yunƙuri na tabbatar da baƙi daga maƙwabta ba su yi katsalandan a zaɓen Nijeriya na 2023 ba, Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) ta ƙwace katunan zaɓe da katin ɗan ƙasa daga hannun baƙin waje guda 6,216 a iyakokin ƙasar guda 21.

Shugaban hukumar ta NIS, CGI Isa Idris Jere ya nuna wa manema labarai katin ɗan ƙasa 3,823 da katin zaɓe 2,393 wanda aka ƙwace daga hannun baki a wasu iyakokin ƙasar nan da suka haɗa da jihohin Nasarawa, Kebbi, Sakwato, Adamawa, Akwa Ibom, Kogi, Yobe, Kwara, Taraba, Filato, Legas, Ogun, Oyo, Zamfara, Jigawa, Edo, Bauchi da Neja da sauran guda uku.

Zabe
Ya bayyana hakan ne a ranar Laraba lokacin da hukumar ta yi ganawar gaggawa da manyan jami’anta da suka haɗa da kodinetoci na rassa da kwamandojinta da ke faɗin Nijeriya a shalkwatanr hukumar a Abuja, kan shirye-shiryen da hukumar za ta gudanar lokacin zaɓe.

ADVERTISEMENT

CGI Jere ya ja kunnen jami’ansa kan su ɗauki ranakun 25 ga watan Fabrairu da 11 ga watan Maris na 2023, a matsayin wata dama ta nuna ƙwarewarsu wajen kula da iyakokin ƙasa da tattara bayanan sirri.

Ya gargaɗe su da cewa duk wani jami’i da aka samu yana haɗa kai domin cin amanar ƙasa za a ɗauke shi a matsayin mai zagon ƙasa kuma zai fuskanci fushin hukumar.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Zabe
Shugaban hukumar ya yi gargaɗin cewa tsauraran matakai na jiran duk wani baƙo da ya yi yunƙurin shiga harkokin zaɓen ƙasar nan. Inda ya yi ƙarin hasken cewa, tun daga lokacin da aka kama waɗannan baki an mayar da su ƙasashensu ne bisa bin dokar Ƙungiyar Bunƙasa Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) kan ‘yancin tafiye-tafiye.

A cewarsa, dokar zaɓe ta 2022 da kuma kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 da aka yi wa kwaskwarima sun ɗora nauyi a kan masu ruwa da tsaki a harkokin zaɓe, musamman ma hukumar NIS, “wannan ne ya sa muka yanke shawarar ɗora wa kwanturololinmu alhakin duk wata gazawa da jami’ansu suka nuna.”
CGI Jere ya nanata aniyar gwamnati ta tabbatar da sahihin zaɓe na gaskiya da adalci, sannan ya buƙaci manyan jami’an hukumar da su ƙara ƙaimi a dukkan iyakokin ƙasar nan lokacin gudanar da ayyukansu domin tabbatar da samun nasarar zaɓe.

Zaɓe
Ya jaddada wajibcin nuna ɗa’a daga jami’ai da kuma jajircewa wajen ci gaba da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.
Ya ce, “A matsayinmu na jami’an gwamnati, an haramta mana nuna ɓangaranci a lokacin zaɓe da kuma bayan zaɓe. Domin haka, hukumar tana amfani da wannan damar wajen wayar da kan dukkan ma’aikata ta hannun kwanturololin bisa buƙatar su ci gaba da kasancewa ‘yan babu ruwanmu gabanin zaɓe da lokacin zaɓe da kuma bayan zaɓe.

“Idan ba mu manta ba cewa rattaba hannu kan dokar zaɓe ta 2022 da shugaban ƙasa ya yi a bara, ya sa hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta fitar da jadawalin lokacin zaɓe, inda ta tsayar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya a ranar 25 ga Fabrairu, 2023, sannan zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun jiha zai biyo baya a ranar 11 ga Maris, 2023.

“Dukkanmu muna sane da irin muhimmancin da gwamnatin tarayya ta bai wa Zaɓen 2023 wanda zai kawo ƙarshen mulkin shekaru 8 na gwamnatin da ke ci yanzu, sannan kuma ƙara cika shekaru 24 da dawowar mulkin dimokuraɗiyya a ƙasarmu mai albarka,” in ji shugaban NIS.

Ya kuma yi gargaɗin cewa duk wani mai zagon ƙasa ko rashin ɗa’a gabanin zaɓe da da lokacin zaɓen da kuma bayan zaɓen zai fuskanci hukunci mai tsanani.

Ya umurci manyan jami’an shige da ficen na ƙananan hukumomi 774 da ke faɗin ƙasar nan da su zurfafa sa ido cikin sirri kan hulɗa da bakin ‘yan ƙasashen waje a dukkan yankunansu domin tabbatar da cewa babu wani baƙo da ya shiga cikin harkokin zaɓen Nijeriya.

Zaɓe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Samar Da Agajin Jin Kai Ga Wadanda Girgizar Kasa Ta Shafa A Syria

Kasar Sin Na Samar Da Agajin Jin Kai Ga Wadanda Girgizar Kasa Ta Shafa A Syria

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.