• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A ƙarfafa Gyare-gyaren Tsarin Tattalin Arziki Da Gwamnatin Tinubu Ke Yi A 2025 – Minista

by Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Za A ƙarfafa Gyare-gyaren Tsarin Tattalin Arziki Da Gwamnatin Tinubu Ke Yi A 2025 – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya tabbatar da cewa shekarar 2025 za ta zama shekarar da za a ƙarfafa gyare-gyaren da ake aiwatarwa ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu, waɗanda tuni suke haifar da sakamako mai kyau a fannonin tsarin tattalin arziki.

 

Idris ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja a wurin taron atisayen shugabanci da gudanarwa wanda gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) ya shirya wa ma’aikatan sa.

  • Kano Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Miƙo Mata Rabonta Na Tsawon Shekaru 25 Daga Shirin NLNG 
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Lashi Takobin Zamowar Kasar Sin Ginshikin Zaman Lafiya Da Hadaka

A jawabin sa, Idris ya jaddada rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen bayyana nasarorin gwamnatin.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

Ya ce: “Babu tantama, ina tabbatar maku da cewa shekarar 2025 za ta ƙarfafa gyare-gyaren Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa, waɗanda tuni suke haifar da sakamako mai kyau a fannoni daban-daban na rayuwar mu ta zamantakewa, tattalin arziki, da siyasa.”

 

Ministan ya jaddada shirin Shugaba Tinubu na aiwatar da manyan gyare-gyaren kuɗi don ƙara wa jihohi da ƙananan hukumomi yawan kuɗaɗen da suke samu domin ciyar da al’ummar Nijeriya gaba, bisa tsarin gaskiya na tarayya.

 

Ya yi kira ga VON, a matsayin sa na gidan watsa labaran ƙasa da ƙasa, da ya bayyana wa da duniya nasarorin da Nijeriya take samu.

 

Ya ce, “Dole ne gidan rediyon Muryar Nijeriya ya sanar wa da duniya cewa Nijeriya ta dawo kan turbar aiki; cewa muna samun nasara a yaƙin da muke yi da ta’addanci, ’yan fashi, da rikicin ƙabilanci; cewa muna ƙarfafa al’ummar mu domin samar da cigaba mai ɗorewa; cewa matasan mu sun samu hanya mafi sauƙi don ilimi mai inganci ta hanyar Asusun Ba da Lamuni na Ilimi na Ƙasa (NEL), sannan kuma abu mafi muhimmanci, cewa ƙasar mu tana kan matakin sauyin makamashi wanda zai tabbatar da wutar lantarki da iskar gas mai ɗorewa don amfani a gidaje da masana’antu.”

 

Ya ƙara da cewa dole ne VON ta tabbatar “ba a bar giɓi ba wajen tattara nasarorin da Nijeriya take samu” ta hanyar rahotanni da nazari da ake watsa wa al’ummar duniya.

 

Idris ya nanata cewa gwamnati za ta ci gaba da amfani da damar da VON take da ita domin yaƙar barazanar labaran ƙarya waɗanda ke barazana ga ƙasar nan a matakin duniya.

 

Ministan ya yi kira ga ƙungiyoyin kafofin watsa labarai kamar VON da su rungumi fasahohin zamani domin su ci gaba da yin gogayya a duniyar watsa labarai, tare da inganta inganci da isar da shirye-shiryen su.

 

Ya kuma yaba wa Darakta-Janar na VON, Malam Jibrin Baba Ndace, tare da masu gudanarwa da ma’aikatan VON bisa sadaukarwar su da hangen nesa wajen tafiyar da hukumar zuwa ga kyakkyawan aiki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Maraba Da Abokai Daga Kasashen Waje Da Suka Kara Mayar Da Hankali Da Ziyartar Kasar

Next Post

‘Yan Nijeriya Sun Biya Kudin Fansa Naira Tiriliyan 2.23 Ga Masu Garkuwa Da Mutane A Cikin watanni 12 – NBS

Related

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

53 minutes ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

4 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

14 hours ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

15 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

17 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

18 hours ago
Next Post
NBS

'Yan Nijeriya Sun Biya Kudin Fansa Naira Tiriliyan 2.23 Ga Masu Garkuwa Da Mutane A Cikin watanni 12 – NBS

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.