ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

by Sadiq
3 years ago
Sarkin Zazzau

Mai martaba Sarkin Zazzau kuma babban mataimaki na kungiyar ‘yan kasuwa, masana’antu, ma’adinai da noma ta Jihar Kaduna (KADCCIMA), Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga yankin Arewa da su tashi tsaye domin magance matsananciyar yunwa da za a iya fuskanta.

Da yake jawabi a wajen bikin karramawa na KADCCIMA karo na 3 da aka gudanar a Kaduna, Sarkin ya ce yankin ba ya bukatar boka da zai shaida musu cewa matsalar yunwa na tafe kuma ya kamata a farka domin noma shi ne ginshikin tattalin arziki.

  • An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar
  • A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

A cewarsa, “Batun matsalar yunwa a shekara mai zuwa, ba ka bukatar boka ya gaya maka abin da zai faru, amma muna addu’a ga Ubangiji Madaukakin Sarki kuma wannan kira ne da ya kamata mutane su yi amfani da wasu hanyoyin da za su bi domin samun mafita, tabbas za ku fuskanci abubuwa wadanda ba a yi tsammani ba.

ADVERTISEMENT

“Ya kamata mu farka daga barcin da muke yi, mu yi abin da za mu iya yi domin ginshikin tattalin arzikinmu ni a ganina shi ne noma, musamman a yankin Arewa, noma ya samu mummunar illa a bana saboda wasu guda biyu, daya ambaliya, na biyu kuma ‘yan bindiga wanda duk abin takaici ne, a yankinmu wanda ke da hadari.”

Ya taya wadanda aka karrama murna, inda ya ce sun bayar da gudunmawa sosai ga tattalin arzikin kasar nan a fannonin rayuwa daban-daban musamman a yankin Arewa.

LABARAI MASU NASABA

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Daga nan sai ya bayyana cewa makarantun gaba da sakandare a duniya ba kyauta ba ne inda ya ce, “Idan ‘yan Nijeriya suna son ilimi mai inganci, sai sun biya, ba wai ina cewa mutane su biye tsadar rayuwa ba saboda wasu kudaden rajistar da muke biya a makarantarmu ta Nijeriya idan har za a biya su, ka kwatanta shi da makarantun da ke ketare, za ka gano cewa muna biyan kudi kadan, idan aka kwatanta da Nijeriya”.

Shi ma da yake jawabi, Gwamna Nasir El-Rufai wanda ya samu wakilcin babban sakataren ma’aikatar kirkire-kirkire ta kasuwanci, Dakta Yusuf Saleh, ya ce a cikin shekaru bakwai da suka gabata gwamnatin Jihar Kaduna ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin ta zuba jari a sassa daban-daban na fannin tattalin arziki. .

Ya ce ma’aikatar kirkire-kirkire ta kasuwanci na bunkasa fasahar matasa don dacewa da al’amuran rayuwa daban-daban.

Shugaban masana’antun Falke, Alhaji Samaila Maigoro, ya bukaci gwamnati da ta zakulo sana’o’in da ake da su tare da karfafa musu gwiwa su kara himmatuwa ta hanyar kayayyakin aiki, horarwa da sauransu.

Shugaban KADCCIMA, Alhaji Sulieman Aliyu, ya ce kungiyar za ta bullo da wani shiri na ba da shawara ga shugabannin ‘yan kasuwa a yankin nan gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
Labarai

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025
Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.