• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai martaba Sarkin Zazzau kuma babban mataimaki na kungiyar ‘yan kasuwa, masana’antu, ma’adinai da noma ta Jihar Kaduna (KADCCIMA), Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, ya yi kira ga yankin Arewa da su tashi tsaye domin magance matsananciyar yunwa da za a iya fuskanta.

Da yake jawabi a wajen bikin karramawa na KADCCIMA karo na 3 da aka gudanar a Kaduna, Sarkin ya ce yankin ba ya bukatar boka da zai shaida musu cewa matsalar yunwa na tafe kuma ya kamata a farka domin noma shi ne ginshikin tattalin arziki.

  • An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar
  • A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

A cewarsa, “Batun matsalar yunwa a shekara mai zuwa, ba ka bukatar boka ya gaya maka abin da zai faru, amma muna addu’a ga Ubangiji Madaukakin Sarki kuma wannan kira ne da ya kamata mutane su yi amfani da wasu hanyoyin da za su bi domin samun mafita, tabbas za ku fuskanci abubuwa wadanda ba a yi tsammani ba.

“Ya kamata mu farka daga barcin da muke yi, mu yi abin da za mu iya yi domin ginshikin tattalin arzikinmu ni a ganina shi ne noma, musamman a yankin Arewa, noma ya samu mummunar illa a bana saboda wasu guda biyu, daya ambaliya, na biyu kuma ‘yan bindiga wanda duk abin takaici ne, a yankinmu wanda ke da hadari.”

Ya taya wadanda aka karrama murna, inda ya ce sun bayar da gudunmawa sosai ga tattalin arzikin kasar nan a fannonin rayuwa daban-daban musamman a yankin Arewa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Daga nan sai ya bayyana cewa makarantun gaba da sakandare a duniya ba kyauta ba ne inda ya ce, “Idan ‘yan Nijeriya suna son ilimi mai inganci, sai sun biya, ba wai ina cewa mutane su biye tsadar rayuwa ba saboda wasu kudaden rajistar da muke biya a makarantarmu ta Nijeriya idan har za a biya su, ka kwatanta shi da makarantun da ke ketare, za ka gano cewa muna biyan kudi kadan, idan aka kwatanta da Nijeriya”.

Shi ma da yake jawabi, Gwamna Nasir El-Rufai wanda ya samu wakilcin babban sakataren ma’aikatar kirkire-kirkire ta kasuwanci, Dakta Yusuf Saleh, ya ce a cikin shekaru bakwai da suka gabata gwamnatin Jihar Kaduna ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin ta zuba jari a sassa daban-daban na fannin tattalin arziki. .

Ya ce ma’aikatar kirkire-kirkire ta kasuwanci na bunkasa fasahar matasa don dacewa da al’amuran rayuwa daban-daban.

Shugaban masana’antun Falke, Alhaji Samaila Maigoro, ya bukaci gwamnati da ta zakulo sana’o’in da ake da su tare da karfafa musu gwiwa su kara himmatuwa ta hanyar kayayyakin aiki, horarwa da sauransu.

Shugaban KADCCIMA, Alhaji Sulieman Aliyu, ya ce kungiyar za ta bullo da wani shiri na ba da shawara ga shugabannin ‘yan kasuwa a yankin nan gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaKadunaNomaSarkin ZazzauTattalin ArzikiYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar

Next Post

Goron Jumu’a

Related

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

46 minutes ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

2 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

16 hours ago
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
Labarai

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

17 hours ago
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.