• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Jefe Mutum Uku Da Dutse Har Su Mutu Har Lahira Kan Laifin Yin Luwadi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
An Gurfanar Da Masu Gadi Kan Zargin Satar ‘Cornflakes’ Din Miliyan 2.1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun Shari’ar Musulunci da ke karamar hukumar Ningi a Jihar Bauchi, ta kama wasu mutum uku da laifin aikata Luwadi don haka ta yanke musu hukuncin kisa ta hanyar jefewa da duwatsu.

Idan za a iya tunawa dai an fara shi ne a ranar 14/6/2022 yayin da dakarun HISBAH ke sintiri a karamar hukumar Ningi karkashin jagorancin Adamu Dan Kafi, inda suka gurfanar da mutane ukun bisa zarginsu da aikata Luwadi.

  • Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi
  • An Kaddamar Da Alkur’ani Da Aka Fassara Zuwa Harshen Igbo A Abuja

Majiyarmu daga kotun shari’ar ta bayyana sunayen wadanda ake zargin da wannan laifin masu suna Abdullahi Abubakar Beti, Kamilu Ya’u da Malam Haruna wadanda kotun shari’ar ta kama da laifin yin Luwadin tare da yanke musu hukuncin.

Dakarun HISBAH din sun shaida wa kotun cewa mutum ukun an kamasu ne su na aikata Luwadi a kauyen Gwada da ke karamar hukumar Ningi.

Bayan da ya saurari dukkanin bayani kan karar, alkalin kotun, Munka’ilu Sabo Ningi, ya ware ranar Laraba 29/6/2022 domin yanke hukunci.

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

Da ya ke yanke hukuncin, alkalin kotun ya ce bisa dogaro da shaidun da suka bayyana a gaban kotun, kotun ta samu mutum ukun da zargin aikata Luwadi don haka ne alkali Munka’ilu Sabo Ningi, ya zartar musu da hukuncin kisa ta hanyar jefewa.

Wadanda za su bakunci lahira ta hanyar jefewa sun kunshi matasa biyu da dattijo guda daya masu suna Abdullahi Abubakar Beti dan shekara 30 a duniya, Kamilu Ya’u 20 da kuma Malam Haruna mai shekara 70 a duniya da aka yanke musu hukuncin bisa dogaro da sashin 134 na dokar jihar Bauchi na shekarar 2001 gami da dogara da tanadin ‘Fiquhussunah Jizu’i’ lamba ta 2 shafi na 362.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiHukunciJefewaKotuLuwadi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ka Yi Murabus Yanzu Ko Mu Tsige Ka – ‘Yan Majalisa Ga Kakakin Majalisar Bauchi

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Jihar Yobe Da Ton 360 Na Kayan Abinci

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

9 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

9 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

10 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

11 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

11 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

11 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Jihar Yobe Da Ton 360 Na Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Jihar Yobe Da Ton 360 Na Kayan Abinci

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.