• English
  • Business News
Monday, May 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti

by Sabo Ahmad
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Za A Rataye Wani Da Ya Yi Wa Budurwa Fyade A Ekiti
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun jihar Ekiti, da ke Ado Ekiti ta yanke wa wani mutum mai kimanin shekara 24, mai suna Segun Iwaetan, hukuncin kisa ta hanyar rataya, saboda kama shi da laifin fyaden da ya yi wa wata makociyarsa mai shekara 20, da kuma kama shi da bindiga guda biyu.

An tuhumi wanda ake zargin ne da laifuka guda bakwai wadanda dukkansu ke da alaka da fyade da mallakar bindiga da kuma zama dan kungiyar asiri.

  • Kotu: Mutane 33 Aka Yi Wa Hukunci Daga 11,000 Da Ake Zargin Sun Aikata Fyade A Nijeriya 

Kamar yadda takardar tuhumar ta nuna, “Segun Iwaetan da Atila Iwaetan (wanda a halin yanzu ya gudu), sun hada baki wajen balle gida da sata a shagon Olayemi Oyerinde, suka kwashi kaya wadanda aka kiyasta kudinsu fiye da naira miliyan 1.8.

Haka kuma wadanda ake zargin ya yi wa wata mace mai kimanin shekara 20 da ke zaune a Odo Ado, Ado Ekiti fyade, an kuma kama shi da laifin mallakar bindiga guda biyu da kuma laifin zama dan kungiyar asiri.

Wadda aka yi wa fyaden ta ce, “wannan da ya yi min fyadrn makocina ne. A wannan rana da zai yi min fyaden, sai ya shigo dakina da tsakar dare, ina kwance ya tashe ni, ya nuna min bindiga kuma ya ce, idan na yi ihu zai harbe ni. Sai ya ce in cire kayana , a nan ne ya yi min fyade. Bayan ya gama, sai ya roke ni cewa in yafe masa. Ni kuma na ce, na ki.”
Dansanda mai gabatar da kara, Albert Adeyemi, ya gabatar da shaidu guda biyar da suka tabbatar da bayanin wadda aka yi wa fyaden. Lauyan wanda ake zargin, bai kira shaida ko daya ba.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Da yake yanke hukunci, mai shari’a Adeniyi Familoni, bayan tabbatar da laifin da ake zargi, ya yanke hukunci kan hada baki wajen aikata laifi da mallakar makami ba bisa ka’ida ba, na shekara 12 a kurkuku, ba tare da zabin tara ba.

“Dangane da batun fyade kuwa, kotun ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai,” Sai kuma shiga kungiyar asiri ta Eiye, alkalin ya gaya wa wanda aka gabatar, cewa “hukunci na karshe shi ne na kisa ta hanyar rataya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharuddan Da ACF Ke Son Duk Mai Neman Ya Gaji Ganduje Ya Cika

Next Post

Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

Sin Da Saudiyya Abokai Ne Na Gaskiya Bisa Manyan Tsare-tsare

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

2027: PDP Ta Mutu, APC Na Shirin Sake Yin Nasara – Martanin Ganduje Ga Lamido 

May 12, 2025
Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 

May 12, 2025
A Koyi Darasi Daga Tarihi

A Koyi Darasi Daga Tarihi

May 11, 2025
Kada A Bata Ran Mahaifiya

Kada A Bata Ran Mahaifiya

May 11, 2025
Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

Sojoji Sun Cafke Dillalan Sayar Da Bindigu A Filato

May 11, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Akasarin Jama’a Da Cudanyar Cinikayya Tare Da Sin Fiye Da Amurka

May 11, 2025
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.