• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Rahotonni
0
Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar lura da yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi hasashen samun guguwa da ruwan sama a faɗin Nijeriya daga Yau Juma’a zuwa Lahadi. A cikin rahoton yanayi da ta fitar a jiya Alhamis a Abuja, NiMet ta yi hasashen iska mai ƙarfi da safe a yau Juma’a a wasu sassan jihohin Kano da Kaduna, tare da ƙarin wata iskar da rana a jihohin Bauchi, da Gombe, da Zamfara, da Sokoto, da Kaduna, da Adamawa, da kuma Taraba.

A yankin tsakiyar arewa kuwa, NiMet ta yi hasashen samun iska mai ƙarfi da ruwan sama da safe a wasu sassan Birnin Tarayya, da Kogi, da Benue, da Neja, da kuma Nasarawa. Da rana kuma ana sa ran guguwar a birnin Tarayya, da Filato, da Nasarawa, da Neja, da Kogi, da Kwara.

  • Ƙananan Hukumomin Kano 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwan Sama — NiMET
  • Daga Yau Litinin Zuwa Laraba Za a Ƙwalla Rana Mai Tsananin Zafi A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

A yankin kudu, an yi hasashen ruwan sama da safe a jihohin Oyo, da Ogun, da Osun, da Edo, da Ondo, da Legas, da Akwa Ibom, da Kuros Riba, da Bayelsa, da Ribas, da kuma Delta, tare da ruwan sama daga baya da rana a dukkan yankin kudu.

A ranar Lahadi, NiMet ta yi hasashen guguwa da safe a wasu sassan jihohin Kebbi, da Kaduna, da Zamfara, tare da guguwar da yamma a jihohin Gombe, da Kaduna, da Bauchi. Bugu da kari, an yi hasashen guguwar da ruwan sama a Birnin Tarayya, da Filato, da Nasarawa, da Neja a lokacin safiya, tare da irin wannan yanayin daga baya da rana a birnin Tarayya, da Filato, da Nasarawa, da kuma Benue. An kuma yi hasashen ruwan sama da safe a wasu sassan jihohin Ondo, da Ogun, da Edo, da Legas, tare da ruwan sama daga baya a cikin rana a jihohin Osun, da Oyo, da Ogun, Ondo, da Legas, da Delta, da Edo, da Ribas, Bayelsa, da Akwa Ibom, da Kuros Riba.

Nimet

Labarai Masu Nasaba

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

NiMet ta yi kira ga jama’a da su ɗauki matakan kariya yayin da ake sa ran iska mai karfi kafin ruwan sama a yankunan da za a iya samun guguwar. Haka kuma, hukumar ta shawarci kamfanonin jiragen sama su samu sabbin rahotanni da hasashen yanayi daga NiMet domin tsara ayyukansu yadda ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GuguwaHasashen YanayiNiMetRuwan SamaTsawaWeather
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa Da Walkiya Suka Haddasa Karancin Mai – NNPCL

Next Post

Amincewar Shugaban Kasa Kawai Muke Jira Mu Yi Kidaya A Nuwamba – NPC

Related

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

6 days ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

6 days ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

7 days ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

4 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

4 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

1 month ago
Next Post
Amincewar Shugaban Kasa Kawai Muke Jira Mu Yi Kidaya A Nuwamba – NPC

Amincewar Shugaban Kasa Kawai Muke Jira Mu Yi Kidaya A Nuwamba – NPC

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.