• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
in Rahotonni
0
Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar lura da yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi hasashen samun guguwa da ruwan sama a faɗin Nijeriya daga Yau Juma’a zuwa Lahadi. A cikin rahoton yanayi da ta fitar a jiya Alhamis a Abuja, NiMet ta yi hasashen iska mai ƙarfi da safe a yau Juma’a a wasu sassan jihohin Kano da Kaduna, tare da ƙarin wata iskar da rana a jihohin Bauchi, da Gombe, da Zamfara, da Sokoto, da Kaduna, da Adamawa, da kuma Taraba.

A yankin tsakiyar arewa kuwa, NiMet ta yi hasashen samun iska mai ƙarfi da ruwan sama da safe a wasu sassan Birnin Tarayya, da Kogi, da Benue, da Neja, da kuma Nasarawa. Da rana kuma ana sa ran guguwar a birnin Tarayya, da Filato, da Nasarawa, da Neja, da Kogi, da Kwara.

  • Ƙananan Hukumomin Kano 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwan Sama — NiMET
  • Daga Yau Litinin Zuwa Laraba Za a Ƙwalla Rana Mai Tsananin Zafi A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

A yankin kudu, an yi hasashen ruwan sama da safe a jihohin Oyo, da Ogun, da Osun, da Edo, da Ondo, da Legas, da Akwa Ibom, da Kuros Riba, da Bayelsa, da Ribas, da kuma Delta, tare da ruwan sama daga baya da rana a dukkan yankin kudu.

A ranar Lahadi, NiMet ta yi hasashen guguwa da safe a wasu sassan jihohin Kebbi, da Kaduna, da Zamfara, tare da guguwar da yamma a jihohin Gombe, da Kaduna, da Bauchi. Bugu da kari, an yi hasashen guguwar da ruwan sama a Birnin Tarayya, da Filato, da Nasarawa, da Neja a lokacin safiya, tare da irin wannan yanayin daga baya da rana a birnin Tarayya, da Filato, da Nasarawa, da kuma Benue. An kuma yi hasashen ruwan sama da safe a wasu sassan jihohin Ondo, da Ogun, da Edo, da Legas, tare da ruwan sama daga baya a cikin rana a jihohin Osun, da Oyo, da Ogun, Ondo, da Legas, da Delta, da Edo, da Ribas, Bayelsa, da Akwa Ibom, da Kuros Riba.

Nimet

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

NiMet ta yi kira ga jama’a da su ɗauki matakan kariya yayin da ake sa ran iska mai karfi kafin ruwan sama a yankunan da za a iya samun guguwar. Haka kuma, hukumar ta shawarci kamfanonin jiragen sama su samu sabbin rahotanni da hasashen yanayi daga NiMet domin tsara ayyukansu yadda ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GuguwaHasashen YanayiNiMetRuwan SamaTsawaWeather
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa Da Walkiya Suka Haddasa Karancin Mai – NNPCL

Next Post

Amincewar Shugaban Kasa Kawai Muke Jira Mu Yi Kidaya A Nuwamba – NPC

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

1 month ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Amincewar Shugaban Kasa Kawai Muke Jira Mu Yi Kidaya A Nuwamba – NPC

Amincewar Shugaban Kasa Kawai Muke Jira Mu Yi Kidaya A Nuwamba – NPC

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

‘Yansanda Sun Tarwatsa Wuraren Haɗa Jabun Taki A Bauchi, An Cafke Mutum 5

May 21, 2025
Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

Kocin Super Eagle Ya Gayyaci Ahmed Musa Buga Gasar Kofin Unity A Landan

May 21, 2025
Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

Tottenham Ta Doke Manchester United A Wasan Karshe Na Europa 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Sabbin Ministoci

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

May 21, 2025
Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.