• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Rika Tuna Wa Da Mijina A Matsayin Gwarzon Gina Rayuwar Matasa –Aisha Buhari

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Za A Rika Tuna Wa Da Mijina A Matsayin Gwarzon Gina Rayuwar Matasa –Aisha Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari ta ce za a tuna da mijinta, shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin shugaban kasa wanda ya bai wa matasa fifiko.

Da ta ke jawabi a Abuja ranar Talata lokacin da ta kaddamar da shirin Health Initiative for Rural Dwellers (HIRD), ta ce shugaban ya fi sha’awar goyon bayan ga shirin gina matasa.

  • Inter Milan Ta Je Wasan Karshe Na Gasar Zakarun Turai
  • Hukumar NDLEA Ta Cafke Mutane 85 Kan Ta’ammuli Da Miyagun Kwayoyi A Gidan Casu A Kano

“Za a tuna da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin wacce ke ba da fifiko ga ci gaban matasa.

“Shugaban kasa yana da kishin NYSC. Goyon bayansa ga wannan tsari ya dogara ne a kan imaninsa ga Nijeriya raya, da kuma godiya ga gudummawar wadannan matasa maza da mata. Don haka, iyalina a kodayaushe suna yi wa ’yan uwa masu hidimar kasa da ke aiki a Daura, Jihar Katsina, zuwa liyafar shugaban kasa a lokacin bukukuwan Sallah,” in ji shi.

Ta kuma yi kira ga masu gudanar da wannan tsari na NYSC da kuma ’yan kungiyar da kada su yi kasa a gwiwa wajen inganta hadin kan kasa ta hanyar samar da ingantacciyar hidima ga al’umma ba tare da la’akari da jiha ko wurin aiki ba.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Buhari ta bayyana cewa an samu nasarar bullo da shirin (HIRD), don haka ofishinta ya yaba da aikin ta hanyar bayar da gudummawar “kayan aikin asibitin tafi da gidanka ga shirin domin bunkasa nasarar kungiyar likitoci.”

Ta ce shirin ya yi tasiri matuka musamman a tsakanin mazauna karkara, wanda ke ci gaba da samun yabo daga ciki da wajen kasar nan.

A nasa bangaren, Darakta Janar na masu yi wa kasa hidima (NYSC) Birgediya Janar Yushau Dogara Ahmed ya ce shirin na HIRD ya samo asali ne daga bukatar magance matsalolin kiwon lafiya da ke addabar talakawa a yankunan karkara a fadin kasar nan.

Ya ce shirin wanda aka fara shi a shekarar 2014, wani dandali ne da jami’an kiwon lafiya da suka hada da likitoci, masu hada magunguna, ma’aikatan jinya, da likitocin hakori, da dai sauransu, suke ba da kiwon lafiya kyauta ga jama’a, musamman talakawan karkara.

Ahmed ya ruwaito cewa kawo yanzu sama da ‘yan Nijeriya miliyan uku ne suka ci gajiyar shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aisha BuhariBuhariMatasaNYSC
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 15 A Abuja

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

Related

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

3 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

11 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

17 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

19 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

21 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

23 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

'Yan Bindiga Sun Kashe Ma'aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.