• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A Rika Tuna Wa Da Mijina A Matsayin Gwarzon Gina Rayuwar Matasa –Aisha Buhari

by Sadiq
2 years ago
Aisha Buhari

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari ta ce za a tuna da mijinta, shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin shugaban kasa wanda ya bai wa matasa fifiko.

Da ta ke jawabi a Abuja ranar Talata lokacin da ta kaddamar da shirin Health Initiative for Rural Dwellers (HIRD), ta ce shugaban ya fi sha’awar goyon bayan ga shirin gina matasa.

  • Inter Milan Ta Je Wasan Karshe Na Gasar Zakarun Turai
  • Hukumar NDLEA Ta Cafke Mutane 85 Kan Ta’ammuli Da Miyagun Kwayoyi A Gidan Casu A Kano

“Za a tuna da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari a matsayin wacce ke ba da fifiko ga ci gaban matasa.

“Shugaban kasa yana da kishin NYSC. Goyon bayansa ga wannan tsari ya dogara ne a kan imaninsa ga Nijeriya raya, da kuma godiya ga gudummawar wadannan matasa maza da mata. Don haka, iyalina a kodayaushe suna yi wa ’yan uwa masu hidimar kasa da ke aiki a Daura, Jihar Katsina, zuwa liyafar shugaban kasa a lokacin bukukuwan Sallah,” in ji shi.

Ta kuma yi kira ga masu gudanar da wannan tsari na NYSC da kuma ’yan kungiyar da kada su yi kasa a gwiwa wajen inganta hadin kan kasa ta hanyar samar da ingantacciyar hidima ga al’umma ba tare da la’akari da jiha ko wurin aiki ba.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Buhari ta bayyana cewa an samu nasarar bullo da shirin (HIRD), don haka ofishinta ya yaba da aikin ta hanyar bayar da gudummawar “kayan aikin asibitin tafi da gidanka ga shirin domin bunkasa nasarar kungiyar likitoci.”

Ta ce shirin ya yi tasiri matuka musamman a tsakanin mazauna karkara, wanda ke ci gaba da samun yabo daga ciki da wajen kasar nan.

A nasa bangaren, Darakta Janar na masu yi wa kasa hidima (NYSC) Birgediya Janar Yushau Dogara Ahmed ya ce shirin na HIRD ya samo asali ne daga bukatar magance matsalolin kiwon lafiya da ke addabar talakawa a yankunan karkara a fadin kasar nan.

Ya ce shirin wanda aka fara shi a shekarar 2014, wani dandali ne da jami’an kiwon lafiya da suka hada da likitoci, masu hada magunguna, ma’aikatan jinya, da likitocin hakori, da dai sauransu, suke ba da kiwon lafiya kyauta ga jama’a, musamman talakawan karkara.

Ahmed ya ruwaito cewa kawo yanzu sama da ‘yan Nijeriya miliyan uku ne suka ci gajiyar shirin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

'Yan Bindiga Sun Kashe Ma'aikatan Ofishin Jakadancin Amurka 4 A Anambra

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.