• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Hada Guiwa Da Hukumomi Don Yaki Da Ta’ammuli Da Miyagun Kwayoyi A Tsakanin ‘Yan Mata – Shugabar MWAN

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
MWAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabar kungiyar Mata Daktoci ta jihar Kaduna kuma ta Kasa (Mai jiran gado), MWAN, Dr. Zainab Muhammad Idris Kwaru ta bayyana cewa, Kungiyar a karkashin jagorancinta za ta maida hankali wajen yaki da ta’ammuli da miyagun kwayoyi ta hanyar hadin guiwa da hukumomin da lamarin ya shafa.

Dr. Kwaru, ta bayyana hakan ne yayin da kungiyar ta kai ziyarar girmamawa ga Mataimakiyar Gwamna Jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe Sabuwa a dakin taro da ke gidan gwamnatin jihar a ranar Alhamis 30 ga watan Nuwamba 2023.

  • Dumamar Yanayi Ta Haddasa Ruwan Saman Ba-zata A Arewa – NiMet
  • Shi Mai Kula Da Babban Aiki Ne 

Tun da farko, Dr. Hadiza Balarabe sabuwa ta nuna farin cikinta na yadda kungiyar ta girmamata ta kawo mata ziyara har gidan Gwamnatin, inda ta ce, itama Mamba ce a kungiyar ta MWAN.

“Babban abinda nafi son kungiyarmu ta mayar da hankali shi ne, la’akari da yadda za a dakile yawaitar ta’ammuli da miyagun kwayoyi a tsakanin ‘yan mata da yaranmu.

“Ya dace, mu kara fadada tunaninmu ta hanyar hadin guiwa da hukumomin da suka dace, kamar NDLEA, don shawo kan wannan kalubale. Hatsari ne babba cikin al’umma, mace tana shaye-shaye, sabida itace uwa mai tarbiyyantar da ‘ya’yanta da al’umma.” Inji Dr. Balarabe.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A nata jawabin, Dr. Zainab Muhammad Kwaru, ta bayyana cewa, Makasudin ziyarar kungiyar itace, kawo gaisuwa ga mai girma mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna, Dr. Hadiza Balarabe sabuwa sannan kuma mu bayyana mata nasarar da muka samu, na zabenmu a matsayin shugabar kungiyar mata daktoci ta kasa, kuma mu nuna mata mun yaba da gudunmawar da ta ba mu na daga lokutanta da kudade da muka yi amfani da su na ganin mun samu wannan nasarar.

Daga nan ne, Dr. Kwaru ta zayyana wa manema labarai wasu daga cikin muhimman shirye-shiryen da kungiyar ke gudanarwa a baya da wadanda take kokarin shiryawa a nan gaba, inda tace, sun hada da shiga cikin al’umma mu bada gudunmawarmu na duba lafiya da basu kulawa na musamman, idan har akwai bukatar tura su manyan asibiti, sai mu yi hakan.

Akwai asibitoci na unguwanni da muka sa mambobinmu suna ziyarta don bada gudunmawa na duba marasa lafiya, muna fadakarwa da wayar da kai acikin al’umma daga bangaren kiwon lafiyar Yara da Mata masu juna-biyu. Wasu lokuta, muna kai kayayyakin agaji ga gidajen kaso ko na gajiyayyu ko na Marayu.

Da take mayar da martani kan batun Mataimakiyar Gwamna na dakile yawaitar ta’ammuli da miyagun kwayoyi a tsakanin yara Mata, Dr. Zainab ta bayyana cewa, daga bangarensu, suna amfani da mambobinsu da ke da kwarewa a fannin kwakwalwa, suna fadakarwa da wayar da kai kan illar ta’ammuli da miyagun kwayoyi.

Ta bayyana cewa, akwai damuwa matuka ganin yadda yara Mata yanzun ke ta’ammuli da miyagun kwayoyi, ganin cewa, itace uwa mai tarbiyyantar da ‘ya’yanta da al’umma baki daya. Lallai wannan barazana ce babba acikin al’ummarmu.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KadunaMWAN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattalin Arzikin Nijeriya Zai Farfado Nan Da Wata 15 – Shettima

Next Post

Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

10 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

13 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

15 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

16 hours ago
Next Post
Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

Faransa Ta Nemi Karin Gurbin Kasuwanci Da Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.