• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana aniyarsa ta ganin ya zamanantar da gidan talbijin ɗin Gwamnatin Tarayya (NTA) ta yadda zai yi goyayya da sauran manyan tashoshin talbijin da ake ji da su a duniya.

Idris ya ce zai ɗora kan shirin maida NTA bisa tsarin aiki cikin sauƙi kuma a zamanance, wato ‘Digital Switch Over’, wanda Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC) ke kan yi.

  • Tsohon Minista Alhaji Bello Maitama Yusuf Ya Rasu Yana Da Shekaru 76 A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Muhimmanta ‘Yancin ‘Yan Jarida – Minista

Ministan ya yi wannan albishir ne a lokacin da ya kai ziyara a hedikwatar NTA, a wani rangadin duba hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar sa da ya ke yi, a ranar Talata.

Ya ce: “Dukkan mu dai mun san irin rawar da NTA ta taka da kuma gudunmawar ta wajen isar da saƙwanni da nishaɗantarwa ga ƙasar mu tsawon shekaru da dama. NTA ta na kan gaba wajen sanar da labarai da ɗumi-ɗumi masu muhimmanci ga ƙasa, sannan ta shahara wajen nuna kyawawan al’adun mu daga ɓangarorin ƙabilun ƙasar nan daban-daban.”

Ya yi tsinkayen cewa aikin babbar kafar yaɗa labarai kamar NTA abu ne da ya zama hantsi leƙa gidan kowa. Kan haka ne ya jinjina wa tashar dangane da yadda su ke gabatar da sahihan labarai, waɗanda ya ce sun taimaka sosai wajen isar da kyawawa kuma ingantattun bayanai ga ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Minista ya ƙara da cewa batun wayar da kan jama’a shi ne babban ginshiƙin da zai ƙarfafa ma’aikatar sa. Kan haka ne ya ce NTA za ta taka muhimmiyar rawa wajen yaɗa kyawawan ɗabi’un wayar da kan jama’a, waɗanda ma’aikatar sa za ta bijiro da su domin ɗora ƙasar nan kan nagartacciyar turbar cigaba mai ɗorewa.

Idris ya ce ya na fatan ganin ya bunƙasa NTA wadda ko bayan saukar sa daga mulki ya kasance ta na goyayya kafaɗa da kafaɗa da manyan gidajen talbijin ɗin da ake tinƙaho da su a duniya yanzu haka a ƙarni na 21.

Ya kuma yi alƙawarin zai samar wa NTA da dukkan kuɗaɗen da ta ke buƙata domin ganin cewa ayyukan ta na tafiya daidai, ba tare da tsaiko ko wata tangarɗa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NTANUJ
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Saudiyya Sun Yi Kunnen Doki A Wasan Sada Zumunta

Next Post

Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

8 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

8 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

9 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

10 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

12 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

13 hours ago
Next Post
Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.