ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 

by Sulaiman
3 years ago
NTA

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana aniyarsa ta ganin ya zamanantar da gidan talbijin ɗin Gwamnatin Tarayya (NTA) ta yadda zai yi goyayya da sauran manyan tashoshin talbijin da ake ji da su a duniya.

Idris ya ce zai ɗora kan shirin maida NTA bisa tsarin aiki cikin sauƙi kuma a zamanance, wato ‘Digital Switch Over’, wanda Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC) ke kan yi.

  • Tsohon Minista Alhaji Bello Maitama Yusuf Ya Rasu Yana Da Shekaru 76 A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Muhimmanta ‘Yancin ‘Yan Jarida – Minista

Ministan ya yi wannan albishir ne a lokacin da ya kai ziyara a hedikwatar NTA, a wani rangadin duba hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar sa da ya ke yi, a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Dukkan mu dai mun san irin rawar da NTA ta taka da kuma gudunmawar ta wajen isar da saƙwanni da nishaɗantarwa ga ƙasar mu tsawon shekaru da dama. NTA ta na kan gaba wajen sanar da labarai da ɗumi-ɗumi masu muhimmanci ga ƙasa, sannan ta shahara wajen nuna kyawawan al’adun mu daga ɓangarorin ƙabilun ƙasar nan daban-daban.”

Ya yi tsinkayen cewa aikin babbar kafar yaɗa labarai kamar NTA abu ne da ya zama hantsi leƙa gidan kowa. Kan haka ne ya jinjina wa tashar dangane da yadda su ke gabatar da sahihan labarai, waɗanda ya ce sun taimaka sosai wajen isar da kyawawa kuma ingantattun bayanai ga ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Minista ya ƙara da cewa batun wayar da kan jama’a shi ne babban ginshiƙin da zai ƙarfafa ma’aikatar sa. Kan haka ne ya ce NTA za ta taka muhimmiyar rawa wajen yaɗa kyawawan ɗabi’un wayar da kan jama’a, waɗanda ma’aikatar sa za ta bijiro da su domin ɗora ƙasar nan kan nagartacciyar turbar cigaba mai ɗorewa.

Idris ya ce ya na fatan ganin ya bunƙasa NTA wadda ko bayan saukar sa daga mulki ya kasance ta na goyayya kafaɗa da kafaɗa da manyan gidajen talbijin ɗin da ake tinƙaho da su a duniya yanzu haka a ƙarni na 21.

Ya kuma yi alƙawarin zai samar wa NTA da dukkan kuɗaɗen da ta ke buƙata domin ganin cewa ayyukan ta na tafiya daidai, ba tare da tsaiko ko wata tangarɗa ba.

NTA
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.