ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 

by Sulaiman
3 years ago
NTA

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana aniyarsa ta ganin ya zamanantar da gidan talbijin ɗin Gwamnatin Tarayya (NTA) ta yadda zai yi goyayya da sauran manyan tashoshin talbijin da ake ji da su a duniya.

Idris ya ce zai ɗora kan shirin maida NTA bisa tsarin aiki cikin sauƙi kuma a zamanance, wato ‘Digital Switch Over’, wanda Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC) ke kan yi.

  • Tsohon Minista Alhaji Bello Maitama Yusuf Ya Rasu Yana Da Shekaru 76 A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Muhimmanta ‘Yancin ‘Yan Jarida – Minista

Ministan ya yi wannan albishir ne a lokacin da ya kai ziyara a hedikwatar NTA, a wani rangadin duba hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar sa da ya ke yi, a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “Dukkan mu dai mun san irin rawar da NTA ta taka da kuma gudunmawar ta wajen isar da saƙwanni da nishaɗantarwa ga ƙasar mu tsawon shekaru da dama. NTA ta na kan gaba wajen sanar da labarai da ɗumi-ɗumi masu muhimmanci ga ƙasa, sannan ta shahara wajen nuna kyawawan al’adun mu daga ɓangarorin ƙabilun ƙasar nan daban-daban.”

Ya yi tsinkayen cewa aikin babbar kafar yaɗa labarai kamar NTA abu ne da ya zama hantsi leƙa gidan kowa. Kan haka ne ya jinjina wa tashar dangane da yadda su ke gabatar da sahihan labarai, waɗanda ya ce sun taimaka sosai wajen isar da kyawawa kuma ingantattun bayanai ga ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Minista ya ƙara da cewa batun wayar da kan jama’a shi ne babban ginshiƙin da zai ƙarfafa ma’aikatar sa. Kan haka ne ya ce NTA za ta taka muhimmiyar rawa wajen yaɗa kyawawan ɗabi’un wayar da kan jama’a, waɗanda ma’aikatar sa za ta bijiro da su domin ɗora ƙasar nan kan nagartacciyar turbar cigaba mai ɗorewa.

Idris ya ce ya na fatan ganin ya bunƙasa NTA wadda ko bayan saukar sa daga mulki ya kasance ta na goyayya kafaɗa da kafaɗa da manyan gidajen talbijin ɗin da ake tinƙaho da su a duniya yanzu haka a ƙarni na 21.

Ya kuma yi alƙawarin zai samar wa NTA da dukkan kuɗaɗen da ta ke buƙata domin ganin cewa ayyukan ta na tafiya daidai, ba tare da tsaiko ko wata tangarɗa ba.

NTA
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Sin Da Saudiyya Na Hadin Gwiwar Gina Sabon Birnin Red Sea Karkashin Hadin Gwiwar Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.