ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Muhimmanta ‘Yancin ‘Yan Jarida – Minista

by Sulaiman
3 years ago
Gwamnatin tarayya

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce gwamnati za ta ƙara himma sosai wajen jaddada ‘yancin ‘yan jarida.

Da ya ke jawabi lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ), Idris ya ce ‘yancin ‘yan jarida da kafafen yaɗa labarai babban ginshiƙi ne wajen samun nasarar dimokuraɗiyya.

  • Ba A Kafa NBC Don Takura Wa Kafafen Yaɗa Labarai Ba – Minista Idris 
  • Gwamnatin Bauchi Ta Kori Shugaban Kungiyar Kwallon Kafa Ta Wikki Tourist

Kan haka ne ya ce gwamnati ta himmatu wajen tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida da kafafen yaɗa labarai.

ADVERTISEMENT

Shugabannin ƙungiyar dai sun kai masa ziyarar ne a ranar Talata, 10 ga Oktoba, 2023.

Ministan ya bayyana manyan ƙalubalen da ‘yan jarida da kafafen yaɗa labarai ke fuskata, waɗanda ya ce sun haɗa da ‘yancin su, samun damar mallakar bayanai da kuma tsaron lafiya da rayukan su.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Ya ce NUJ ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da ɗorewar dimokiraɗiyya.

Ya hore su da a haɗa hannu domin samun ci gaba. Ya ce: “Muradin da mu ka sa a gaba shi ne mu tabbatar da cewa ‘yan jarida su na gudanar da aikin su ba tare da fargabar wata barazana ga lafiya ko rayuka ba.”

Sai dai kuma ya yi tsokacin cewa duk da ‘yancin ‘yan jarida abu ne mai matuƙar daraja a fagen yaɗa labarai, to kuma abu ne mai muhimmanci a ga cewa ana yin taka-tsantsan tare da bayar da labarai sahihai ga ‘yan Nijeriya.

Ya jaddada cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da gaske ta ke yi wajen kula da ‘yancin ‘yan jarida, tare da ƙoƙarin ganin sun riƙa gudanar da aikin su ba tare da tsangwama ko wani cikas ba.

A jawabin sa, Shugaban NUJ na ƙasa, Mista Chris Isiguzo, ya fayyace ƙalubalen da ‘yan jarida ke fuskanta, waɗanda su ka haɗa da ‘yancin ‘yan jarida, damar ba su bayanai a ma’aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati, tsaron lafiya da rayukan su da kuma matsalolin na yau da kullum na tsadar rayuwa.

Ya ce ya na yi wa ministan kallon wani nagartaccen tsanin da za a taka domin a kai ƙololuwar wurin da za a iya magance waɗannan matsaloli.

Gwamnatin tarayya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Shugabannin Kasashen Duniya Na Cike Da Kyakkyawan Fata Game Da Taron Raya Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

Shugabannin Kasashen Duniya Na Cike Da Kyakkyawan Fata Game Da Taron Raya Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.