• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Kwace Lasisin Kamfanonin Wutar Lantarkin Nijeriya – Minista

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Za Mu Kwace Lasisin Kamfanonin Wutar Lantarkin Nijeriya – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Lantarki, Bayo Adelabu, ya yi barazanar kwace lasisin kamfanonin rarraba wuta na Discos, yana mai cewa ba za a lamunci yanayin da suke saka mutane na karancin wutar ba.

Ministan, wanda ya wallafa sakon barazanar a shafinsa na X a ranar Laraba.

  • NiMet Ta Yi Hasashen Bullar Zazzabin Cizon Sauro A Watan Maris Da Afrilu
  • Sin Da Aljeriya Na Fatan Bunkasa Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki

Ya ce ya damu matuka da tabarbarewar samar da wuta da ake fama da rashin ta a fadin kasar nan.

“Don haka ne ma na kira shugabannin Kamfanin Rarraba Lantarki na Abuja (AEDC) da na Ibadan (IBEDC), da kuma shugaban Kamfanin Samar da Lantarki na Nijeriya TCN don yin wata ganawa mai muhimmanci,” in ji ministan.

Ya ce ya kira taron ne don tattaunawa kan yadda ake matukar fama da matsalar samun wuta a wadannan yankunan da kuma nemo mafita.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yanzu haka dai ana matukar fama da karancin wuta a wasu sassan Nijeriya, musamman babban birnin tarayya, Abuja a daidai lokacin da yanayin zafi ke kara kunno kai.

“Abin takaici ne ganin yadda ake samun raguwar wutar lantarki duk da kokarin da ake yi na inganta lamarin.

“Ma’aikatar Lantarki ta matsa lamba kan Kamfanonin da ke Samar da Wutar (GENCOs) don inganta ayyukansu, lamarin da ya sa aka samu karuwar samar da wuta zuwa sama da megawat 4000,” a cewar Ministan.

Sai dai Mista Adelabu ya bayyana cewa duk da wannan ci gaba da ake samu, wasu kamfanonin sun gaza rarraba wutar da TCN ke bayarwa yadda ya kamata.

Ya kuma koka kan yadda yawan barnar kayayyakin samar da wutar da ake yi ke kara ta’azzara matsalar a Abuja da Benin da Fatakwal da kuma Ibadan.

Minista Adelabu ya sha alwashin cewa daga yanzu zai kama dukkan kamfanonin rarraba wutar da alhaki idan har ba su yi abin da ya dace ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

NiMet Ta Yi Hasashen Bullar Zazzabin Cizon Sauro A Watan Maris Da Afrilu

Next Post

Sabuwar Cuta Ta Hallaka Mutane 30 A Gombe

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

7 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

19 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

1 day ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

1 day ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Next Post
Sabuwar Cuta Ta Hallaka Mutane 30 A Gombe

Sabuwar Cuta Ta Hallaka Mutane 30 A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.