• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci -Kwamitin Rabon Abinci A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Za Mu Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci -Kwamitin Rabon Abinci A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin da gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri, ya dora wa alhakin raba kayayyakin abinci da rage radadi, biyo bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi, ya bayyana tsare-tsaren ganin rabon ya kai ga mutanen da suka fi bukata.

Da yake jawabi jim kadan da kammala ganawar da mambobin kwamitin suka yi a Yola a ranar Litinin, sakataren gwamnatin jihar Awwal Bamanga Tukur, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin, ya ce za su tabbatar da gaskiya da adalci a rabon.

  • Mutane Sun Daka Wa Kayan Abinci Wawa A Bayelsa Saboda Yunwa
  • Tinubu Ya Umarci Rage Yawan Masu Zuwa Taron UNGA Don Rage Kashe Kudin Gwamnati 

Ya ci gaba da cewa “shirin zai shafi harkokin jama’a ta kowane bangare, musamman tafiye-tafiye, rage kudaden farashin kayayyakin abinci da kashi 50 bisa dari, a daukacin cibiyoyin kada kuri’a 266, a fadin jihar.

“Shirin zai kawo saukin tafiye-tafiye ga ma’aikata, ‘yan makaranta, masu kananan karfi da matafiya da ke shigowar jiha, kan haka mun samar da motocin bas-bas 10 daga kamfanin Innoson a kan kudi naira biliyan 1.06”.

Tukur, ya ce manufar shirin shi ne kawo sauki ga wahalhalun da jama’a ke ciki, ya ce “mutane mabukata kamar; matan da mazajensu suka mutu, matan da aurensu ya mutu, nakasassun mutane, makarantun kwana da kungiyoyin mata da matasa su za su amfana da shirin, za mu tabbatar kowa ya amfani” in ji Bamanga.

Labarai Masu Nasaba

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Haka kuma sakataren gwamnatin jihar Awwal Tukur, ya ce gwamnatin jihar ta karbi tallafin naira miliyan dubu biyu, daga gwamnatin tarayya, kari kan tirelan biyar na shinkafa, yabce ita ma gwamnatin jihar ta samar da tirela 50, na shinkafa da masara.

“Bisa umarni, za mu tabbatar da jama’a sun samu sauki, za mu tabbatar farashinmu ya karya farashin abinci a kasuwa, za mu sayarda karamin buhu a kan kudi naira dubu 10, ba kamar yadda yake a kasuwa dubu 20 ba” in ji Bamanga.

Shugaban kwamitin ya ce kwamitin yana da masu sa ido game yadda shirin zai ci gaba da gudana, ya roke ‘yan jaridu da su rika bibiyan aikin kwamitn, ana dai tsamammin za a fara aikin a ranar Laraba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane Sun Daka Wa Kayan Abinci Wawa A Bayelsa Saboda Yunwa

Next Post

Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

Related

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

8 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

9 hours ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

13 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

13 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

15 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

16 hours ago
Next Post
Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

Sharuda 5 Da Tinubu Ya Gindaya Wa Ministocinsa

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.