• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 

by Sadiq
3 years ago
CBN

A yayin da ake ci gaba da fuskantar tsaiko wajen tura kudi ta intanet da kuma amfani da na’urar cirar kudii ta PoS, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya musanta bayanan da ake yadawa cewar ya bayar da umarnin katse hanyoyin tura kudi ta intanet a lokacin zaben da za a yi a ranar Asabar.

Labarin ya jefa fargaba a zukatan mutane har ta kai mutane sun fara rige-rigen zuwa kasuwanni domin tanadar abubuwan bukata kamar abinci da man fetur domin ajiye su a gida har zuwa lokacin da za a kammala zabe.

  • Zabe: ‘Yan Siyasa Sun Boye Tsofaffin Kudi Sama Da Biliyan 500 Ba Su Mayar CBN Ba – Bawa
  • INEC Ta Haramtawa Masu Zabe Amfani Da Wayar Salula Yayin Kada Kuri’a A Rumfar Zabe

Labarin da ya karade ko ina musamman a kafar WhatsApp.

A ranar Laraba ne dai CBN ya karyata rahotannin da ake ta yadawa ba tare da yin karin haske kan batun ba.

A sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter, CBN ya ce babu gaskiya a labarin katse Intanet kuma ba daga wurinsa sanarwar ta fito ba.

LABARAI MASU NASABA

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

Canjin kudi a Nijeriya dai ya janyo cece-kuce a bangarori da dama tun bayan fara aiwatar da tsarin a Disambar 2022.

Lamarin dai ya sa an yi ta samun bayanai na karya kan tsarin sakamakon rashin fitowar Babban Bankin Nijeriya na kin yi wa mutane bayani dalla-dalla game da manufarsa ta bijiro da shi.

Rarrabuwar kan da aka samu kan batun saka wa’adin mayar da tsofaffin takardun kudi zuwa ga batun ci gaba da amfani da su da kuma bayanan da aka rika samu daga bankuna sun jefa jama’a cikin fargaba da kuma rashin sanin alkiblar da za su bi.

Daga cikin irin wadannan bayanai masu janyo rudani da aka yi ta yadawa a baya-bayan nan akwai wanda ke cewa za a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000 har zuwa 1 ga watan Mayun 2023.

Sai dai kotun kolin da ke sauraren shari’ar da gwamnonin APC suka shigar ta sake dage zaman har zuwa ranar 1 ga watan Maris mai zuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojojin somaliya
Manyan Labarai

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025
Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

October 12, 2025
An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
Manyan Labarai

An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

October 12, 2025
Next Post
Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

LABARAI MASU NASABA

Sojojin somaliya

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

October 13, 2025
Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina

October 12, 2025
Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 12, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”

October 12, 2025
An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje

An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje

October 12, 2025
Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba

October 12, 2025
Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace

October 12, 2025
An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro

October 12, 2025
Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan

October 12, 2025
Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?

October 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.