• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ake ci gaba da fuskantar tsaiko wajen tura kudi ta intanet da kuma amfani da na’urar cirar kudii ta PoS, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya musanta bayanan da ake yadawa cewar ya bayar da umarnin katse hanyoyin tura kudi ta intanet a lokacin zaben da za a yi a ranar Asabar.

Labarin ya jefa fargaba a zukatan mutane har ta kai mutane sun fara rige-rigen zuwa kasuwanni domin tanadar abubuwan bukata kamar abinci da man fetur domin ajiye su a gida har zuwa lokacin da za a kammala zabe.

  • Zabe: ‘Yan Siyasa Sun Boye Tsofaffin Kudi Sama Da Biliyan 500 Ba Su Mayar CBN Ba – Bawa
  • INEC Ta Haramtawa Masu Zabe Amfani Da Wayar Salula Yayin Kada Kuri’a A Rumfar Zabe

Labarin da ya karade ko ina musamman a kafar WhatsApp.

A ranar Laraba ne dai CBN ya karyata rahotannin da ake ta yadawa ba tare da yin karin haske kan batun ba.

A sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter, CBN ya ce babu gaskiya a labarin katse Intanet kuma ba daga wurinsa sanarwar ta fito ba.

Labarai Masu Nasaba

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

Canjin kudi a Nijeriya dai ya janyo cece-kuce a bangarori da dama tun bayan fara aiwatar da tsarin a Disambar 2022.

Lamarin dai ya sa an yi ta samun bayanai na karya kan tsarin sakamakon rashin fitowar Babban Bankin Nijeriya na kin yi wa mutane bayani dalla-dalla game da manufarsa ta bijiro da shi.

Rarrabuwar kan da aka samu kan batun saka wa’adin mayar da tsofaffin takardun kudi zuwa ga batun ci gaba da amfani da su da kuma bayanan da aka rika samu daga bankuna sun jefa jama’a cikin fargaba da kuma rashin sanin alkiblar da za su bi.

Daga cikin irin wadannan bayanai masu janyo rudani da aka yi ta yadawa a baya-bayan nan akwai wanda ke cewa za a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000 har zuwa 1 ga watan Mayun 2023.

Sai dai kotun kolin da ke sauraren shari’ar da gwamnonin APC suka shigar ta sake dage zaman har zuwa ranar 1 ga watan Maris mai zuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNHada-Hadar KudiIntanet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zabe: ‘Yan Siyasa Sun Boye Tsofaffin Kudi Sama Da Biliyan 500 Ba Su Mayar CBN Ba – Bawa

Next Post

Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

28 minutes ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

2 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

14 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

18 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

22 hours ago
Next Post
Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.