ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zabe: CBN Ya Musanta Shirin Katse Hada-Hadar Kudi Ta Intanet 

by Sadiq
4 years ago
CBN

A yayin da ake ci gaba da fuskantar tsaiko wajen tura kudi ta intanet da kuma amfani da na’urar cirar kudii ta PoS, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya musanta bayanan da ake yadawa cewar ya bayar da umarnin katse hanyoyin tura kudi ta intanet a lokacin zaben da za a yi a ranar Asabar.

Labarin ya jefa fargaba a zukatan mutane har ta kai mutane sun fara rige-rigen zuwa kasuwanni domin tanadar abubuwan bukata kamar abinci da man fetur domin ajiye su a gida har zuwa lokacin da za a kammala zabe.

  • Zabe: ‘Yan Siyasa Sun Boye Tsofaffin Kudi Sama Da Biliyan 500 Ba Su Mayar CBN Ba – Bawa
  • INEC Ta Haramtawa Masu Zabe Amfani Da Wayar Salula Yayin Kada Kuri’a A Rumfar Zabe

Labarin da ya karade ko ina musamman a kafar WhatsApp.

ADVERTISEMENT

A ranar Laraba ne dai CBN ya karyata rahotannin da ake ta yadawa ba tare da yin karin haske kan batun ba.

A sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter, CBN ya ce babu gaskiya a labarin katse Intanet kuma ba daga wurinsa sanarwar ta fito ba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Canjin kudi a Nijeriya dai ya janyo cece-kuce a bangarori da dama tun bayan fara aiwatar da tsarin a Disambar 2022.

Lamarin dai ya sa an yi ta samun bayanai na karya kan tsarin sakamakon rashin fitowar Babban Bankin Nijeriya na kin yi wa mutane bayani dalla-dalla game da manufarsa ta bijiro da shi.

Rarrabuwar kan da aka samu kan batun saka wa’adin mayar da tsofaffin takardun kudi zuwa ga batun ci gaba da amfani da su da kuma bayanan da aka rika samu daga bankuna sun jefa jama’a cikin fargaba da kuma rashin sanin alkiblar da za su bi.

Daga cikin irin wadannan bayanai masu janyo rudani da aka yi ta yadawa a baya-bayan nan akwai wanda ke cewa za a ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000 har zuwa 1 ga watan Mayun 2023.

Sai dai kotun kolin da ke sauraren shari’ar da gwamnonin APC suka shigar ta sake dage zaman har zuwa ranar 1 ga watan Maris mai zuwa.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

Wajibi Ne A Gudanar Da Bincike Na Gaskiya Game Da Lamarin Bututun “Nord Stream”

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.