ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Majalisar Dinkin Duniya Da ECOWAS Sun Yi Sabon Gargadi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
ECOWAS

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Majalisar Dinkin Duniya (UN) da Kungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) sun gargadi Nijeriya game da rikicin zaben 2023.

Yayin da UN ta yi gargadin cewa, idan har abubuwa suka ci gaba da tabarbarewa a Nijeriya, to za a samu mummunan sakamako ga zaman lafiya da kwamciyar hankali a kasar baki daya, sannan kungiyar ECOWAS ta ce idan aka samu tashin hankali a Nijeriya, babu wata kasa a yankin Yammacin Afirka da za ta iya daukar ‘yan gudun hijirar Nijeriya.

  • Yadda Ake Kafa Kamfanin Burodi
  • An Watsa Shirin Bidiyo Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Bazara A Wurare Daban Daban Na Duniya

Sun dai yi wannan gargadin ne a garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato a wurin wani taro na bayar da horon sasantawa da hulda da hadakan kungiyoyin da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka fito daga yankin arewa ta tsakiya da arewa maso gabas kan dakile rikice-rikicen zaben 2023.
An bayar da rahoton cewa sama da mutum 30 ne suka rasa rayukansu, sannan da dama sun jikkata sakamakon rikice-rikicen zaben 2023 a wasu sassan Nijeriya.
Haka kuma an sa sha kai hare-hare a ofisoshin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), musamman a yankin kudu maso gabashin Nijeriya, wadanda yawancinsu suna da alaka da haramtacciyar kungiyar nan mai fafatukar kafa kasar Biafara (IPOB), lamarin da ya kai ga kashe ma’aikatan INEC da jami’an tsaro da dama.
Da take jawabi a wurin taron, wakiliyar ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da yammacin Afirka, Sa’adatu Sha’abu ta ce, “Idan har al’amura suka ci gaba da yin tsami a Nijeriya, za a samu mummunan sakamako ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkan yankin yammacin Afirka.”
Jami’in tsare-tsare na kungiyar ECOWAS, wanda ya kasance mai shiga tsakani Brown Odigie ya ja kunnen masu ruwa da tsaki kan gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da lumana.
Odigie ya kasance wakilin kwamishinan kungiyar ECOWAS kan harkokin siyasa, zaman lafiya da kuma tsaro, Abel Fatau ya bukaci dukkan ‘yan takara da jam’iyyunsu da su martaba yarjejeniyar zaman lafiya da suka sanya wa hannu da kuma ka’idojin zaben 2023.
Ya ce, “Wannan wani sasanci ne da ake yawan yi a kasashen da ke cikin kungiyar ECOWAS. Muna yin wannan lamari a Nijeriya ne, saboda Nijeriya ta kasance babbar mamba a kungiyar ECOWAS.
“Nijeriya na da dimbin al’umma. Zaben na iya haifar da rikici idan har ba a gudanar da shi yadda ya kamata ba. Kuma idan har aka samu rikici, zai iya shafar sauran kasashe makwabta saboda dinbin jama’an da Nijeriya take da su. Ina mai tabbatar muku da cewa babu wata kasa a cikin kungiyar ECOWAS da ke da karfin daukar ‘yan gudun hijira daga Nijeriya.”
Sakataren gamayyar kungiyoyin na kasa, Yusuf Dantalle ya bayyana cewa ‘yan saiyasa sukan shiga halin kaka-ni-ka-yi a lokacin da suka yi rashin nasara, saboda makudan kudaden da suke kashewa a zabe.

ADVERTISEMENT
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.