• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023: Majalisar Dinkin Duniya Da ECOWAS Sun Yi Sabon Gargadi

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Zaben 2023: Majalisar Dinkin Duniya Da ECOWAS Sun Yi Sabon Gargadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Majalisar Dinkin Duniya (UN) da Kungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) sun gargadi Nijeriya game da rikicin zaben 2023.

Yayin da UN ta yi gargadin cewa, idan har abubuwa suka ci gaba da tabarbarewa a Nijeriya, to za a samu mummunan sakamako ga zaman lafiya da kwamciyar hankali a kasar baki daya, sannan kungiyar ECOWAS ta ce idan aka samu tashin hankali a Nijeriya, babu wata kasa a yankin Yammacin Afirka da za ta iya daukar ‘yan gudun hijirar Nijeriya.

  • Yadda Ake Kafa Kamfanin Burodi
  • An Watsa Shirin Bidiyo Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Bazara A Wurare Daban Daban Na Duniya

Sun dai yi wannan gargadin ne a garin Jos, Babban Birnin Jihar Filato a wurin wani taro na bayar da horon sasantawa da hulda da hadakan kungiyoyin da sauran masu ruwa da tsaki wadanda suka fito daga yankin arewa ta tsakiya da arewa maso gabas kan dakile rikice-rikicen zaben 2023.
An bayar da rahoton cewa sama da mutum 30 ne suka rasa rayukansu, sannan da dama sun jikkata sakamakon rikice-rikicen zaben 2023 a wasu sassan Nijeriya.
Haka kuma an sa sha kai hare-hare a ofisoshin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), musamman a yankin kudu maso gabashin Nijeriya, wadanda yawancinsu suna da alaka da haramtacciyar kungiyar nan mai fafatukar kafa kasar Biafara (IPOB), lamarin da ya kai ga kashe ma’aikatan INEC da jami’an tsaro da dama.
Da take jawabi a wurin taron, wakiliyar ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da yammacin Afirka, Sa’adatu Sha’abu ta ce, “Idan har al’amura suka ci gaba da yin tsami a Nijeriya, za a samu mummunan sakamako ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkan yankin yammacin Afirka.”
Jami’in tsare-tsare na kungiyar ECOWAS, wanda ya kasance mai shiga tsakani Brown Odigie ya ja kunnen masu ruwa da tsaki kan gudanar da zaben 2023 cikin kwanciyar hankali da lumana.
Odigie ya kasance wakilin kwamishinan kungiyar ECOWAS kan harkokin siyasa, zaman lafiya da kuma tsaro, Abel Fatau ya bukaci dukkan ‘yan takara da jam’iyyunsu da su martaba yarjejeniyar zaman lafiya da suka sanya wa hannu da kuma ka’idojin zaben 2023.
Ya ce, “Wannan wani sasanci ne da ake yawan yi a kasashen da ke cikin kungiyar ECOWAS. Muna yin wannan lamari a Nijeriya ne, saboda Nijeriya ta kasance babbar mamba a kungiyar ECOWAS.
“Nijeriya na da dimbin al’umma. Zaben na iya haifar da rikici idan har ba a gudanar da shi yadda ya kamata ba. Kuma idan har aka samu rikici, zai iya shafar sauran kasashe makwabta saboda dinbin jama’an da Nijeriya take da su. Ina mai tabbatar muku da cewa babu wata kasa a cikin kungiyar ECOWAS da ke da karfin daukar ‘yan gudun hijira daga Nijeriya.”
Sakataren gamayyar kungiyoyin na kasa, Yusuf Dantalle ya bayyana cewa ‘yan saiyasa sukan shiga halin kaka-ni-ka-yi a lokacin da suka yi rashin nasara, saboda makudan kudaden da suke kashewa a zabe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASGargadiZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ake Kafa Kamfanin Burodi

Next Post

Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 days ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

3 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

3 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 week ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

1 week ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
Next Post
Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

Yadda Sin Ta Nuna Kyakkyawar Alkiblar Yaki Da Mummunan Tasirin Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

July 28, 2025
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

July 28, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

July 28, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

July 28, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

July 28, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

July 28, 2025
An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

July 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.