• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023 Ne Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya –Gbajabiamila

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben 2023 Ne Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya –Gbajabiamila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya ce zaben 2023 ya kasance mafi inganci zabe da aka taba gudanarwa a tarihin Nijeriya.

Shugaban majalisar, ya lura ce an samu ci gaba a kokarin kasar nan na tabbatar da sahihin zabe.

  • 2023: Jihohin Da INEC Ta Bayyana Sakamakon Zaben Gwamnoni
  • Magoya Bayan Peter Obi Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja Kan Zaben 2023

Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban majalisar ya tabbatar da cewa majalisar za ta tabbatar da amincewa da kudirin dokar hukumar laifuffukan zabe kafin karewar wa’adinta a watan Yuni.

Gbajabiamila ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja yayin da yake maraba da takwarorinsa da suka dawo daga zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha da aka kammala.

“Mun tabbatar an samu ci gaban da aka samu a kokarin da muke yi na tabbatar da zaben da za mu yi alfahari da shi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

A cewar Gbajabiamila, gyaran dokar zabe da majalisar dokokin kasar nan ta 9 ta yi, ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta harkokin zabe ta hanyar amfani da na’urorin fasaha don saukaka tantance masu kada kuri’a da yada sakamakon zabe.

“A kowace sabuwar kakar zabe, muna kara fahimtar bangarorin da ke bukatar sauye-sauye don tabbatar da samun kyakkyawan sakamako a lokaci na gaba.  Dole ne a ci gaba da gudanar da gyare-gyaren da ya dace.  A matsayin matakin farko da ya dace, ya kamata Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta hada kai tare da masu ruwa da tsaki don samar da sahihiyar hanyar tantance tsarin zaben. Wannan ya zama dole don sanar da karin gyare-gyare da ingantawa,” in ji shi.

A halin da ake ciki kuma, Gbajabiamila ya lura cewa kudurorin gyara kundin tsarin mulkin kasar nan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya wa hannu a makon jiya za su ciyar da tarayyar Nijeriya gaba tare da kusantar da kasar wajen cimma burinta na kasa baki daya.

“Lokacin da muka fara aikin duba kundin tsarin mulki a majalisar wakilai ta 9, na ce wannan wata dama ce ta samar da kundin tsarin mulki wanda zai warware matsaloli da dama da ke damun al’ummarmu da kuma kawo mana cikas.

“A makon da ya gabata, Mai Girma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya rattaba hannu kan gyare-gyaren kundin tsarin mulkin kasar nan da majalisar dokoki ta kafa da kuma majalisun jihohin kasar nan suka amince da su.

“Wadannan gyare-gyaren tsarin mulkin sun hada da gyare-gyaren da za a iya dauka don kira da kuma yadda ake gudanar da harkokin mulkin Nijeriya, musamman game da batun raba madafun iko ga jihohi da karfafa shari’a da majalisa a matakin kasa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Femi GbajabiamilaZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Zama Kasa Mafi Saurin Karuwar Albarkatun Gandun Daji

Next Post

Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

Related

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

3 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

11 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

17 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

19 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

21 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

23 hours ago
Next Post
Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.