• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023 Ne Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya –Gbajabiamila

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben 2023 Ne Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya –Gbajabiamila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya ce zaben 2023 ya kasance mafi inganci zabe da aka taba gudanarwa a tarihin Nijeriya.

Shugaban majalisar, ya lura ce an samu ci gaba a kokarin kasar nan na tabbatar da sahihin zabe.

  • 2023: Jihohin Da INEC Ta Bayyana Sakamakon Zaben Gwamnoni
  • Magoya Bayan Peter Obi Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja Kan Zaben 2023

Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban majalisar ya tabbatar da cewa majalisar za ta tabbatar da amincewa da kudirin dokar hukumar laifuffukan zabe kafin karewar wa’adinta a watan Yuni.

Gbajabiamila ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja yayin da yake maraba da takwarorinsa da suka dawo daga zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha da aka kammala.

“Mun tabbatar an samu ci gaban da aka samu a kokarin da muke yi na tabbatar da zaben da za mu yi alfahari da shi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

A cewar Gbajabiamila, gyaran dokar zabe da majalisar dokokin kasar nan ta 9 ta yi, ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta harkokin zabe ta hanyar amfani da na’urorin fasaha don saukaka tantance masu kada kuri’a da yada sakamakon zabe.

“A kowace sabuwar kakar zabe, muna kara fahimtar bangarorin da ke bukatar sauye-sauye don tabbatar da samun kyakkyawan sakamako a lokaci na gaba.  Dole ne a ci gaba da gudanar da gyare-gyaren da ya dace.  A matsayin matakin farko da ya dace, ya kamata Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta hada kai tare da masu ruwa da tsaki don samar da sahihiyar hanyar tantance tsarin zaben. Wannan ya zama dole don sanar da karin gyare-gyare da ingantawa,” in ji shi.

A halin da ake ciki kuma, Gbajabiamila ya lura cewa kudurorin gyara kundin tsarin mulkin kasar nan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya wa hannu a makon jiya za su ciyar da tarayyar Nijeriya gaba tare da kusantar da kasar wajen cimma burinta na kasa baki daya.

“Lokacin da muka fara aikin duba kundin tsarin mulki a majalisar wakilai ta 9, na ce wannan wata dama ce ta samar da kundin tsarin mulki wanda zai warware matsaloli da dama da ke damun al’ummarmu da kuma kawo mana cikas.

“A makon da ya gabata, Mai Girma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya rattaba hannu kan gyare-gyaren kundin tsarin mulkin kasar nan da majalisar dokoki ta kafa da kuma majalisun jihohin kasar nan suka amince da su.

“Wadannan gyare-gyaren tsarin mulkin sun hada da gyare-gyaren da za a iya dauka don kira da kuma yadda ake gudanar da harkokin mulkin Nijeriya, musamman game da batun raba madafun iko ga jihohi da karfafa shari’a da majalisa a matakin kasa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Femi GbajabiamilaZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Zama Kasa Mafi Saurin Karuwar Albarkatun Gandun Daji

Next Post

Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

9 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Zaben 2023

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.