• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben 2023 Ne Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya –Gbajabiamila

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Zaben 2023 Ne Mafi Inganci A Tarihin Nijeriya –Gbajabiamila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila, ya ce zaben 2023 ya kasance mafi inganci zabe da aka taba gudanarwa a tarihin Nijeriya.

Shugaban majalisar, ya lura ce an samu ci gaba a kokarin kasar nan na tabbatar da sahihin zabe.

  • 2023: Jihohin Da INEC Ta Bayyana Sakamakon Zaben Gwamnoni
  • Magoya Bayan Peter Obi Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja Kan Zaben 2023

Hakan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban majalisar ya tabbatar da cewa majalisar za ta tabbatar da amincewa da kudirin dokar hukumar laifuffukan zabe kafin karewar wa’adinta a watan Yuni.

Gbajabiamila ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja yayin da yake maraba da takwarorinsa da suka dawo daga zaben gwamna da na ‘yan majalisar jiha da aka kammala.

“Mun tabbatar an samu ci gaban da aka samu a kokarin da muke yi na tabbatar da zaben da za mu yi alfahari da shi,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

A cewar Gbajabiamila, gyaran dokar zabe da majalisar dokokin kasar nan ta 9 ta yi, ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta harkokin zabe ta hanyar amfani da na’urorin fasaha don saukaka tantance masu kada kuri’a da yada sakamakon zabe.

“A kowace sabuwar kakar zabe, muna kara fahimtar bangarorin da ke bukatar sauye-sauye don tabbatar da samun kyakkyawan sakamako a lokaci na gaba.  Dole ne a ci gaba da gudanar da gyare-gyaren da ya dace.  A matsayin matakin farko da ya dace, ya kamata Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta hada kai tare da masu ruwa da tsaki don samar da sahihiyar hanyar tantance tsarin zaben. Wannan ya zama dole don sanar da karin gyare-gyare da ingantawa,” in ji shi.

A halin da ake ciki kuma, Gbajabiamila ya lura cewa kudurorin gyara kundin tsarin mulkin kasar nan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sanya wa hannu a makon jiya za su ciyar da tarayyar Nijeriya gaba tare da kusantar da kasar wajen cimma burinta na kasa baki daya.

“Lokacin da muka fara aikin duba kundin tsarin mulki a majalisar wakilai ta 9, na ce wannan wata dama ce ta samar da kundin tsarin mulki wanda zai warware matsaloli da dama da ke damun al’ummarmu da kuma kawo mana cikas.

“A makon da ya gabata, Mai Girma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya rattaba hannu kan gyare-gyaren kundin tsarin mulkin kasar nan da majalisar dokoki ta kafa da kuma majalisun jihohin kasar nan suka amince da su.

“Wadannan gyare-gyaren tsarin mulkin sun hada da gyare-gyaren da za a iya dauka don kira da kuma yadda ake gudanar da harkokin mulkin Nijeriya, musamman game da batun raba madafun iko ga jihohi da karfafa shari’a da majalisa a matakin kasa,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Femi GbajabiamilaZaben 2023
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Zama Kasa Mafi Saurin Karuwar Albarkatun Gandun Daji

Next Post

Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

Related

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Kasashen Ketare

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

28 minutes ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

20 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

20 hours ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

23 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

23 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

2 days ago
Next Post
Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Sin A Cikin Rahoton Amurka Game Da Hakkin Dan Adam Na 2022 Na Cike Da Karairayin Siyasa Da Son Zuciya

LABARAI MASU NASABA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.