• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnan Osun: PDP Ta Zargi APC Da Shirin Amfani Da ‘Yan Bangar Siyasa

by Abubakar Abba
3 years ago
in Labarai
0
Zaben Gwamnan Osun: PDP Ta Zargi APC Da Shirin Amfani Da ‘Yan Bangar Siyasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP a jihar Osun ta zargi jam’iyyar APC mai mulki a jihar bisa son yin amfani da ‘yan bangar siyasa domin lashe zaben gwamna da za a yi a ranar 16 ga watan Julin 2022.

PDP ta bukaci Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Julius Alawari Okoro da kuma DIG Johnson Babatunde Kokum, da su gaggauta dakile aukuwar yunkurin na APC.

  • Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba – Matawalle
  • Gwamnatin Buhari Za Ta Yi Mai Yiwuwa Wajen Tabbatar Da Tsaro A Kasar Nan – Malami

PDP ta kara da cewa bisa bayanan da ta samu, ta na kuma zargin APC da yunkurin shigo da mutane dauke da malamai domin ta tayar da hargitsi a lokacin zaben.

Shugaban kwanitin riko na PDP a jihar, Akindele Adekunle ne, ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar a jihar, inda ya yi zargin cewa APC za ta shigo da ‘yan bangar siyasar ne daga jihar Legas wadanda kuma za a kama wa dakuna a otal-otal.

A cewar Adekunle, “Muna da bayanan APC ta tura irin wadandan ‘yan bangar siyasar zuwa shiyoyin jihar har da a shiyyar Iwo inda aka kashe jami’in PDP.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

Sai dai, a martanin da kakakin yakin neman zaben gwamnan APC, Sunday Akere, ya mayar ga PDP ya ce, zargin na PDP abin dariya ne domin PDP ta riga ta hango ba za ta samu nasara a zaben ba.

Ya kara da da cewa, tuni an san APC jam’iyya ce da ba ta goyon bayan dukkan nau’in tayar da rikici.

A karshe, ya yi kira ga daukacin ‘yan jihar da suka kai munzalin jefa kuri’a da su fito kwansu da kwarkwatarsu domin su sake zabar gwamnan jihar, Adegboyega Oyetola don yin tazarce a karo na biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Bangar SiyasaAPCJihar OsunPDPSiyasaZaben Gwamna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Muhimmanta Tsaro Ba – Matawalle

Next Post

Haramtattun Kudaden Da Ke Yawo A Afirka Sun Karu Zuwa Dala Biliyan 80– CDD

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

7 minutes ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

24 minutes ago
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
Labarai

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

41 minutes ago
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
Labarai

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

2 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

4 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

5 hours ago
Next Post
Haramtattun Kudaden Da Ke Yawo A Afirka Sun Karu Zuwa Dala Biliyan 80– CDD

Haramtattun Kudaden Da Ke Yawo A Afirka Sun Karu Zuwa Dala Biliyan 80– CDD

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.