• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Zaben Gwamnoni: INEC Ta Gargadi Jam’iyyun Siyasa Kan Tada Tarzoma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta gargadi jam’iyyun siyasa da magoya bayansu gabanin shiga zaben gwamnoni da za a yi ranar Asabar.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya yi wannan gargadin a ranar Talata a Abuja yayin wani kwamitin tuntubar hukumomin tsaro kan harkokin zabe.

  • ‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya
  • Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin ‘Yan Bindiga

Yayin da ake sa ran gudanar da zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha da za a yi ranar Asabar, INEC ta gargadi jam’iyyun siyasa da magoya bayansu da kada su shiga duk wani tashin hankali da zai iya kawo cikas ga zaben.

Ya kuma yi kira ga jam’iyyun siyasa da su dauki kansu a matsayin masu ruwa da tsaki a zabe mai zuwa ta yadda za su tunkari shi a matsayin takara ba yaki ba.

Shugaban na INEC ya kara da cewa an yi wa jami’an tsaro bayanai dalla-dalla kan yadda zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi da suka hada da wuraren da aka gudanar da rumfunan zabe da wuraren tattara sakamakon zabe tare da bayyana kwarin gwiwar cewa za su yi aikinsu da kwarewa kamar yadda aka saba a baya.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

“Saboda haka, muna sa ran shirin tura sojoji tare da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro, leken asiri.

“A jiya ne hukumar ta gudanar da wani taron tattaunawa da dukkan kwamishinonin zabe, inda muka duba shirye-shiryen zaben. Baya ga fasahar zabe, kayan aiki da sauran batutuwa da dama, an kuma tattauna batun tsaro,” in ji Yakubu.

Shugaban INEC ya kara da cewa hukumar a shirye take ta tunkari duk wasu shari’o’in da suka shafi laifukan zabe, ya kuma yabawa sufeto-janar na ‘yansanda bisa umarnin da ya bayar a baya-bayan nan cewa, har yanzu irin wadannan shari’o’in na hannun ‘yansanda.

“Ya kamata su guji tashe-tashen hankula da za su iya kawo cikas ga zaben ko kuma kawo cikas ga tsaron ma’aikatanmu, masu sa ido, kafafen yada labarai,” in ji shi.

“Hukumar ta samu kwarin gwiwa bisa umarnin da babban sufeton ‘yansanda ya bai wa jihohi.

“Muna sa ran karbar kararrakin da aka shigar. Nan take za mu kafa wata tawaga ta lauyoyi da za ta tunkari irin wadannan shari’o’i.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GargadiINECSiyasaZaben Gwamnoni
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Takaran Gwamna 8 Sun Mara Wa Gwamnan Gombe Baya

Next Post

Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

7 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

8 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

10 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

11 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

12 hours ago
Next Post
Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna

Mutum 10 Sun Rasu, Da Dama Sun Jikkata A Wani Sabon Hari A Kudancin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.