Shugaban Hukumar Zabe ta kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ya gargadi ma’aikatan hukumar da aka tura gudanar da aikin zaben gwamnan jihar Osun, a yau Asabar cewar su kwana da sanin cewa sun karbi rantsuwa don samun nasarar gudanar da zaben.
Jam’iyyu 15 ne za su fafata a zaben na yau, inda masu fashin baki a harkar siysar jihar suka yi hasashen cewa, zaben zai kasance ne a tsakanin APC da kuma PDP.
- ‘Yan Sanda Sun Kara Cafke Wani Fursuna Da Ya Arce Daga Gidan Yarin Kuje A Katsina
- Bayan Daukar Rafinha, Barcelona Ta Taya Lewandowski
A cikin sanarwar da Yakubu ya fitar a jiya Juma’a, ya umarci duk ma’aikatan hukumar da aka tura gudanar da zaben da su tabbatar da sun nuna kwarewarsu don a gudanar da sahihin zaben na gwamna.
A cewarsa, “‘Yan Nijeriya da kuma alummar jihar ta Osun mu za su zarga in har ba mu yi abin da ya kamata ba a yayin gudanar da zaben.
“Za su kuma lura da yadda muka tafiyar da zaben da sakamakon zaben da kuma matakan da muka dauka don gudanar da zaben.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp