• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Shugabanni: Sabon Rikici Ya Kunno Kai A PDP

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin nan ne jam’iyyar PDP ta gudanar da zaben shugabannin a matakin kananan hukumomi, sai dai kuma zabe ya bar baya da kura wanda ya haifar da wani sabon rikici a cikin jam’iyyar PDP bayan zargin da ake yi wa mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Ambasada Illiya Damagum da sakataren gudanar da zabe, Umar Bature na sauya sakamakon zaben da aka gudanar a jihohi.

 

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa, Kola Ologbondiyan, wanda kuma ya caccaki Damagum da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, kan rubuta wa kotun daukaka kara da ke Jihar Ribas cewa jam’iyyar za ta ci gaba da daukaka kara kan ‘yan majalisar dokokin Jihar Ribas 27 da suka sauya sheka, sabanin matakin da aka dauka kan mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a Mista Ajibade.

  • Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar
  • Kudirin Wa’adin Shekaru 6 Ga Shugaban Kasa Ya Tsallake Karatu Na Farko

Tsohon sakataren yada labaran jam’iyyar ya ce mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa ya saba wa kundin tsarin mulkin jam’iyyar ne ta hanyar daukar wannan mataki ba tare da bin umarnin mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa ba, wanda a cewarsa sashi na 42 (1) ya bai wa jam’iyyar damar zabar wakili kan harkokin shari’a.

 

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ologbondiyan ya yi kira ga sauran mambobin kwamitin ayyuka na kasa wadanda ba su goyi bayan matakin da Damagum ya dauka ba, su kira taron gaggawa na kwamitin gudanarwar domin kada kuri’ar rashin amincewa da shugaban riko na kasa da kuma sakataren jam’iyyar na kasa.

 

Karar mai lamba PHC/2177/CS/2024, ta ta’allaka ne kan takaddamar sauya sheka da ‘yan majalisar dokokin Jihar Ribas su 27 suka yi zuwa jam’iyyar APC a ranar 11 ga Disamba, 2023.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a kwanakin baya ne jam’iyyar PDP ta gudanar da taronta na mazabu da na kananan hukumomi. Babban taron a wasu jihohin kamar Kogi da Binuwai, Katsina ya haifar da zazzafar muhawara a tsakanin shugabannin jam’iyyar a jihohin.

 

Sai dai da yake tattaunawa a gidan talabijin na Arise, yayin da yake mayar da martani kan lamarin Jihar Ribas, Ologbondiyan ya ce, “Lokacin da na fara ganin waccan wasikar, ban yarda ba, amma ba zato ba tsammani shugaban rikon jam’iyyar na kasa da kuma sakatarenmu na kasa sun rubuta wasika wanda ya saba wa sashe na 42 (1) na kundin tsarin mulkin jam’iyyar, wanda ya ba da ikon zabar wakili na bangaren shari’a ga duk wani lamarin da ya shafi shari’a na kasa kan mai ba da shawara a harkokin shari’a na kasa.

 

“Cewa mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Ambasada Illiya Damagum da Sanata Anyanwu za su gabatar da wata takarda zuwa kotun daukaka kara, ban yarda ba. Amma cikin sa’o’i 24 na tabbatar da hakan, wannan wani irin babban abin kunya ne?

 

“A wannan hali ne muka samu jam’iyyarmu. Kuma ban ma ga wani abin mamaki ba, musamman a Jihar Benuwai a jam’iyyarmu, Cif Sesgu Angba yana fitowa ya ba da labarin abubuwan da ke faruwa a kusan kowace jiha ta tarayya, inda aka yi kokarin murde zaben shugabannin a matakin kananan hukumomi, wanda ake zargin sakataren shirya taron, Bature da Damagum da Sanata Anyanwu suna aikatawa.

 

“Ban fahimci abin da ake nufi da manufar wannan duka ba, amma wannan abin damuwa ne. Kuma tun jiya shugabannin jam’iyyar suka yi ta kira da tattaunawa a tsakanin juna suna tambaya cewa, “Wannan shi ne karshe? Wannan ne irin shugabanci da muka tsinci kanmu a ciki?

 

“Na sha fada a baya cewa abun kunya ne mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa ya gurfana a gaban kwamitin gudanarwa da kwamitin zartarwa da kuma kwamitin amintattun jam’iyya kan saba wat sarin mulkin jam’iyyar PDP.

“Don haka zai gurfana a gaban kotu ne kan dukkan sassan jam’iyyar, saboda kawai yana son ya zauna a kan mukaminsa ko ta halin ya ya,” in ji shi.

A cewar Ologbondiyan, akwai shirin ruguza jam’iyyar, lamarin da ke faruwa a Jihar Ribas, wanda ya nuna cewa mukaddashin shugaban jam’iyyar yana tare da ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike.

Ologbondiyan ya kuma zargin Damagum da sauya jadawalin gudanar da zaben ba tare da izini ba, wanda ya tsawaita gudanar da taron kwamitin gudanarwa har zuwa watan Satumba.

A karshen makon da ya gabata ne, ‘yan majalisar tarayya na jam’iyyar adawa suka zargi Damagum da Anyanwu da shirya makarkashiyar dagula muradun jam’iyyar PDP a Jihar Ribas.

‘Yan majalisar karkashin jagorancin Hon. Ikenga Ugochinyere, sun ce Damagun da Anyawu sun nuna adawa da matakin da PDP ta dauka na mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa na ganin an kawar da ‘yan majalisar da ke goyon bayan Wike da suka koma jam’iyyar APC tare da hana su cutar da muradun PDP da kuma yiwuwar tsige Gwamna Siminalayi Fubara a matsayin gwamnan Ribas.

Ugochinyere ya bayyana cewa, babbar kotun Jihar Ribas ta bayar da umarni a ranar 8 ga watan Yuli, 2024, inda ta hana manyan jami’an jihar yin mu’amala da ‘yan majalisar da suka sauya sheka.

Sai dai ya yi zargin Dakta J.Y. Musa, na shigar da kara kan wannan umarni, duk da adawar da mai bai wa PDP shawara kan harkokin shari’a ya nuna.

Ya ce, “Mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a na kasa, wanda tsarin jam’iyyar ya ba shi ikon kare muradun jam’iyyar PDP, ya riga ya janye karar a ranar 24 ga Yuli, 2024, bisa la’akari da irin illar da zai iya yi wa jam’iyyar.

“A wani lamari mai ban mamaki da ya faru a ranar 15 ga Agusta, 2024, Damagum da Anyanwu sun aika da wasika zuwa kotun daukaka kara da ke Fatakwal, inda suka nesanta kansu da hukuncin kotu, tare da yin zagon kasa ga matakin da mai ba da shawara kan harkokin shari’a ya dauka,” in ji Ugochinyere.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kira Taron Binciken Manufofin Gaggauta Aikin Raya Yankin Yammacin Kasar

Next Post

Sin Na Kira Da A Gudanar Da Tsarin Sa Ido Mai Inganci Mai Zaman Kan Sa Ga Batun Zubar Da Dagwalon Ruwan Fukushima 

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

6 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Sin Na Kira Da A Gudanar Da Tsarin Sa Ido Mai Inganci Mai Zaman Kan Sa Ga Batun Zubar Da Dagwalon Ruwan Fukushima 

Sin Na Kira Da A Gudanar Da Tsarin Sa Ido Mai Inganci Mai Zaman Kan Sa Ga Batun Zubar Da Dagwalon Ruwan Fukushima 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.