• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Za Mu Sabunta Ɗakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsofaffin Ɗaliban Sashen Harsunan Nijeriya da Kimiyyar Harshe na Jami’ar Bayero ‘yan ajin shekarar karatu ta 2011 zuwa 2015 sun sha alwashin sabunta ɗakin karatu na sashen wanda aka fi sani da Ɗakin Karatu Na Farfesa MAZ Sani.

Shugaban tawagar tsofaffin ɗaliban, Alh. Hassan Baita Ubawaru, ne ya bayyana haka yayin da ya ke miƙa wasu sababbin injinan naɗar takardu (Photocopy) guda uku da ya gwangwaje sashen nasu a madadin ɗaliban a matsayin gudunmawarsu don sauƙaƙa harkokin koyo da koyarwa a sashen a ranar Alhamis 02, ga watan Nuwambar 2023.

Injinan Nadar Takardu Uku Da Tsofaffin Daliban Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Suka Suka Ba BUK
Injinan Naɗar Takardu Uku Da Tsofaffin Ɗaliban Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Suka Suka Ba BUK
  • Jami’ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu
  • Tsohon Shugaban Jam’iar Bayero Ta Kano, Farfesa Ibrahim Umar Ya Rasu

Da yake miƙa injinan, Alh. Hassan Baita, wanda shi ne shugaban taron sada zumunci na ‘yan ajin shekarar 2015 kuma wanda ya ɗauki nauyan sayan injinan ya ce, wannan somun-taɓi ne kuma lokaci bayan lokaci za a ke irin waɗannan ayyuka don bunƙasa wannan sashe.

Tsofaffin Daliban Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Yayin Mika Injinan Nadar Takardu A BUK
Tsofaffin Ɗaliban Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya Yayin Miƙa Injinan Naɗar Takardu A BUK

A nasa jawabin, tsohon Sakataren Ƙungiyar Hausa ta Jami’ar Bayero, Muhammad Bashir Amin, ya bayyana ƙudurinsu na bunƙasa sashen ta hanyar bijiro da ayyukan da za su ciyar da sashen gaba, ya kuma buƙaci malamai da su ƙara kyautata alaƙarsu da ɗalibansu su ja su a jika, su ɗauke su tamkar ‘ya’yan da suka haifa, saboda hakan zai ƙara yi wa ɗaliban ƙaimi wajen tunawa da su bayan Allah ya ɗaukaka su a rayuwa.

Shugaban Sashen, Farfesa Isah Mukhtar, ya godewa ɗaliban da suka yi wannan hoɓɓasa da abun arziƙi a lokacin da ya ke shugabantar sashen, ya kuma bayyana cewa haƙiƙa irin wannan tallafi zai taimaka musu su tsallake tantancewar hukumar kula da Jami’o’i ta ƙasa da za ta yi wa sashen a shekara mai zuwa, wanda gaza samar da kayan koyo da koyarwa da kayan gudanar da aiki ka iya kaiwa ga samun babbar matsalar da zata iya kaiwa ga rufe sashen baki ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Taron ya samu halartar mataimakin shugaban tsangayar fasaha da nazarin addinin musulunci da malaman sashen yayin bikin miƙa injinan.

Mahalarta taron daga ɓangaren malamai da ɗalibai sun jinjinawa ƙoƙarin tsofaffin ɗaliban na samar da injinan, sun kuma gode musu da fatan Allah ya yalwata arziƙinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUKHassan Baita UbawaruHausaJami'ar BayerokanoUniversity
ShareTweetSendShare
Previous Post

Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa

Next Post

Yadda Rakiyar Gwamnan Kano Ga Tagwayen da ke Manne Da Juna Ta Dauki Hankalin Al’umma

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

12 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

14 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

15 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

16 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

17 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

18 hours ago
Next Post
Yadda Rakiyar Gwamnan Kano Ga Tagwayen da ke Manne Da Juna Ta Dauki Hankalin Al’umma

Yadda Rakiyar Gwamnan Kano Ga Tagwayen da ke Manne Da Juna Ta Dauki Hankalin Al'umma

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.