• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Bude Sabon Shafi A Barcelona, Cewar Gundogan

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Zan Bude Sabon Shafi A Barcelona, Cewar Gundogan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kyaftin din Manchester City Ilkay Gundogan ya koma kungiyar Barcelona, bayan karewar kwanturaginsa a karshen wannan wata kamar yadda kungiyar ta kasar Spaniya ta bayyana.

Manchester City ta gabatar wa Gundogan mai shekara 32, sabon kwanturagi amma ana jin cewa ya daidaita a kan wata yarjejeniya da ta fi tsoka ta tsawon shekara uku da zakarun na kasar Sifaniya.

  • Kante Ya Yarda Ya Koma Saudiya Da Taka Leda

Kocin Manchester City Pep Guardiola yana alla-alla ya ci gaba da aiki tare da Gundogan, wanda jigo ne a nasarar kungiyar wajen lashe kofi uku a kakar wasan da ta gabata.

Gundogan, dan kasar Jamus mai buga wasa a tsakiya ya buga wasa 51 a kakar wasanni ta 2022 zuwa 2023, inda ya ci kwallo 11 ciki har da kwallayen da ya ci a wasan karshe na gasar FA Cup, inda Manchester City ta doke Manchester United, a ciki har da kwallon da aka ci mafi sauri a tarihin kofin FA bayan dakika 13 kacal.

Ya buga wasa tsawon minti 90 a karawar karshe ta Gasar cin Kofin Zakarun Turai, inda Man City ta ci Inter Milan 1-0, abin da ya sa ta dora a kan nasarorinta na gasar Firimiya da kofin FA a kakar bana.

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Gundogan ya shiga kungiyar Manchester City daga Borussia Dortmund a kan kudin da aka ba da rahoto sun kai fam miliyan 20 a shekara ta 2016, kuma ya buga wa kungiyar wasanni 304, ya ci kwallo 60 sannan ya taimaka aka zura guda 40 a raga.

A tsawon shekara bakwai da ya kwashe a filin kwallo na Etihad, ya ci kofi 14 – Gasar Firimiya biyar da Gasar Zakarun Turai daya da Kofin FA biyu sai Kofin EFL guda hudu da kuma Community Shields biyu.

A farkon kakar 2022 zuwa 2023 ne Man City ta nada shi matsayin kyaftin bayan dan wasan tsakiyar Brazil Fernandinho ya bar kungiyar kuma zamansa kyaftin ya kawo wa kungiyar gagarumar nasara.

A karshe dai, lamarin ya kare cikin wani sassaukan lissafi daga yadda Man City ke kallon lamarin saboda suna son Gundogan ya ci gaba da zama amma kuma sun girmama matakin da ya dauka na son tafiya.

Guardiola ya yi ta zazzaga wa Gundogan kalmomin yabo musamman a makonnin
karshe na kakar wasannin mai cike da tarihi a kungiyar ta Manchester City sai dai City ba za ta iya kashe ko nawa ba ne, don kawai tana so ta ci gaba da zama da Gundogan.

Zakarun na Ingila da Turai sun yi masa tayin kwanturagin shekara daya da yiwuwar karin kakar wasanni amma Barcelona ta yi masa tayin da ya kunshi karin shekara daya a kan na Manchester City.

Gundogan yana da shekara 32, kuma zakakurin dan wasa a City, yana sane da cewa ‘yan kwallo kafar ne za su iya gasa da shi kuma Man City, a matsayin kungiyar da ta yi nasarar cin kofi uku, suna kan sharafinsu.
‘Yan wasa a yanzu na son zuwa su buga kwallo da Guardiola.

Kungiyar za ta iya samun zaratan ‘yan baiwa, kuma ko Kobacic, yana daf da yin haka sai dai Man City cikin bege za ta rika tunawa da Gundugan tamkar dai David Silva da Yaya Toure da kuma Vincent Kompany.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bala Kauran Bauchi Ya Gwangwaje Alhazan Bauchi Da Kyautar Riyal Dari Uku-Uku

Next Post

Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

2 days ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

4 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

5 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

6 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

6 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

1 week ago
Next Post
Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.