ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Bude Sabon Shafi A Barcelona, Cewar Gundogan

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Gundogan

Kyaftin din Manchester City Ilkay Gundogan ya koma kungiyar Barcelona, bayan karewar kwanturaginsa a karshen wannan wata kamar yadda kungiyar ta kasar Spaniya ta bayyana.

Manchester City ta gabatar wa Gundogan mai shekara 32, sabon kwanturagi amma ana jin cewa ya daidaita a kan wata yarjejeniya da ta fi tsoka ta tsawon shekara uku da zakarun na kasar Sifaniya.

  • Kante Ya Yarda Ya Koma Saudiya Da Taka Leda

Kocin Manchester City Pep Guardiola yana alla-alla ya ci gaba da aiki tare da Gundogan, wanda jigo ne a nasarar kungiyar wajen lashe kofi uku a kakar wasan da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Gundogan, dan kasar Jamus mai buga wasa a tsakiya ya buga wasa 51 a kakar wasanni ta 2022 zuwa 2023, inda ya ci kwallo 11 ciki har da kwallayen da ya ci a wasan karshe na gasar FA Cup, inda Manchester City ta doke Manchester United, a ciki har da kwallon da aka ci mafi sauri a tarihin kofin FA bayan dakika 13 kacal.

Ya buga wasa tsawon minti 90 a karawar karshe ta Gasar cin Kofin Zakarun Turai, inda Man City ta ci Inter Milan 1-0, abin da ya sa ta dora a kan nasarorinta na gasar Firimiya da kofin FA a kakar bana.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Gundogan ya shiga kungiyar Manchester City daga Borussia Dortmund a kan kudin da aka ba da rahoto sun kai fam miliyan 20 a shekara ta 2016, kuma ya buga wa kungiyar wasanni 304, ya ci kwallo 60 sannan ya taimaka aka zura guda 40 a raga.

A tsawon shekara bakwai da ya kwashe a filin kwallo na Etihad, ya ci kofi 14 – Gasar Firimiya biyar da Gasar Zakarun Turai daya da Kofin FA biyu sai Kofin EFL guda hudu da kuma Community Shields biyu.

A farkon kakar 2022 zuwa 2023 ne Man City ta nada shi matsayin kyaftin bayan dan wasan tsakiyar Brazil Fernandinho ya bar kungiyar kuma zamansa kyaftin ya kawo wa kungiyar gagarumar nasara.

A karshe dai, lamarin ya kare cikin wani sassaukan lissafi daga yadda Man City ke kallon lamarin saboda suna son Gundogan ya ci gaba da zama amma kuma sun girmama matakin da ya dauka na son tafiya.

Guardiola ya yi ta zazzaga wa Gundogan kalmomin yabo musamman a makonnin
karshe na kakar wasannin mai cike da tarihi a kungiyar ta Manchester City sai dai City ba za ta iya kashe ko nawa ba ne, don kawai tana so ta ci gaba da zama da Gundogan.

Zakarun na Ingila da Turai sun yi masa tayin kwanturagin shekara daya da yiwuwar karin kakar wasanni amma Barcelona ta yi masa tayin da ya kunshi karin shekara daya a kan na Manchester City.

Gundogan yana da shekara 32, kuma zakakurin dan wasa a City, yana sane da cewa ‘yan kwallo kafar ne za su iya gasa da shi kuma Man City, a matsayin kungiyar da ta yi nasarar cin kofi uku, suna kan sharafinsu.
‘Yan wasa a yanzu na son zuwa su buga kwallo da Guardiola.

Kungiyar za ta iya samun zaratan ‘yan baiwa, kuma ko Kobacic, yana daf da yin haka sai dai Man City cikin bege za ta rika tunawa da Gundugan tamkar dai David Silva da Yaya Toure da kuma Vincent Kompany.

Gundogan
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.