ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Bude Sabon Shafi A Barcelona, Cewar Gundogan

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Gundogan

Kyaftin din Manchester City Ilkay Gundogan ya koma kungiyar Barcelona, bayan karewar kwanturaginsa a karshen wannan wata kamar yadda kungiyar ta kasar Spaniya ta bayyana.

Manchester City ta gabatar wa Gundogan mai shekara 32, sabon kwanturagi amma ana jin cewa ya daidaita a kan wata yarjejeniya da ta fi tsoka ta tsawon shekara uku da zakarun na kasar Sifaniya.

  • Kante Ya Yarda Ya Koma Saudiya Da Taka Leda

Kocin Manchester City Pep Guardiola yana alla-alla ya ci gaba da aiki tare da Gundogan, wanda jigo ne a nasarar kungiyar wajen lashe kofi uku a kakar wasan da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Gundogan, dan kasar Jamus mai buga wasa a tsakiya ya buga wasa 51 a kakar wasanni ta 2022 zuwa 2023, inda ya ci kwallo 11 ciki har da kwallayen da ya ci a wasan karshe na gasar FA Cup, inda Manchester City ta doke Manchester United, a ciki har da kwallon da aka ci mafi sauri a tarihin kofin FA bayan dakika 13 kacal.

Ya buga wasa tsawon minti 90 a karawar karshe ta Gasar cin Kofin Zakarun Turai, inda Man City ta ci Inter Milan 1-0, abin da ya sa ta dora a kan nasarorinta na gasar Firimiya da kofin FA a kakar bana.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Gundogan ya shiga kungiyar Manchester City daga Borussia Dortmund a kan kudin da aka ba da rahoto sun kai fam miliyan 20 a shekara ta 2016, kuma ya buga wa kungiyar wasanni 304, ya ci kwallo 60 sannan ya taimaka aka zura guda 40 a raga.

A tsawon shekara bakwai da ya kwashe a filin kwallo na Etihad, ya ci kofi 14 – Gasar Firimiya biyar da Gasar Zakarun Turai daya da Kofin FA biyu sai Kofin EFL guda hudu da kuma Community Shields biyu.

A farkon kakar 2022 zuwa 2023 ne Man City ta nada shi matsayin kyaftin bayan dan wasan tsakiyar Brazil Fernandinho ya bar kungiyar kuma zamansa kyaftin ya kawo wa kungiyar gagarumar nasara.

A karshe dai, lamarin ya kare cikin wani sassaukan lissafi daga yadda Man City ke kallon lamarin saboda suna son Gundogan ya ci gaba da zama amma kuma sun girmama matakin da ya dauka na son tafiya.

Guardiola ya yi ta zazzaga wa Gundogan kalmomin yabo musamman a makonnin
karshe na kakar wasannin mai cike da tarihi a kungiyar ta Manchester City sai dai City ba za ta iya kashe ko nawa ba ne, don kawai tana so ta ci gaba da zama da Gundogan.

Zakarun na Ingila da Turai sun yi masa tayin kwanturagin shekara daya da yiwuwar karin kakar wasanni amma Barcelona ta yi masa tayin da ya kunshi karin shekara daya a kan na Manchester City.

Gundogan yana da shekara 32, kuma zakakurin dan wasa a City, yana sane da cewa ‘yan kwallo kafar ne za su iya gasa da shi kuma Man City, a matsayin kungiyar da ta yi nasarar cin kofi uku, suna kan sharafinsu.
‘Yan wasa a yanzu na son zuwa su buga kwallo da Guardiola.

Kungiyar za ta iya samun zaratan ‘yan baiwa, kuma ko Kobacic, yana daf da yin haka sai dai Man City cikin bege za ta rika tunawa da Gundugan tamkar dai David Silva da Yaya Toure da kuma Vincent Kompany.

Gundogan
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.