ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Bude Sabon Shafi A Barcelona, Cewar Gundogan

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Gundogan

Kyaftin din Manchester City Ilkay Gundogan ya koma kungiyar Barcelona, bayan karewar kwanturaginsa a karshen wannan wata kamar yadda kungiyar ta kasar Spaniya ta bayyana.

Manchester City ta gabatar wa Gundogan mai shekara 32, sabon kwanturagi amma ana jin cewa ya daidaita a kan wata yarjejeniya da ta fi tsoka ta tsawon shekara uku da zakarun na kasar Sifaniya.

  • Kante Ya Yarda Ya Koma Saudiya Da Taka Leda

Kocin Manchester City Pep Guardiola yana alla-alla ya ci gaba da aiki tare da Gundogan, wanda jigo ne a nasarar kungiyar wajen lashe kofi uku a kakar wasan da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Gundogan, dan kasar Jamus mai buga wasa a tsakiya ya buga wasa 51 a kakar wasanni ta 2022 zuwa 2023, inda ya ci kwallo 11 ciki har da kwallayen da ya ci a wasan karshe na gasar FA Cup, inda Manchester City ta doke Manchester United, a ciki har da kwallon da aka ci mafi sauri a tarihin kofin FA bayan dakika 13 kacal.

Ya buga wasa tsawon minti 90 a karawar karshe ta Gasar cin Kofin Zakarun Turai, inda Man City ta ci Inter Milan 1-0, abin da ya sa ta dora a kan nasarorinta na gasar Firimiya da kofin FA a kakar bana.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Gundogan ya shiga kungiyar Manchester City daga Borussia Dortmund a kan kudin da aka ba da rahoto sun kai fam miliyan 20 a shekara ta 2016, kuma ya buga wa kungiyar wasanni 304, ya ci kwallo 60 sannan ya taimaka aka zura guda 40 a raga.

A tsawon shekara bakwai da ya kwashe a filin kwallo na Etihad, ya ci kofi 14 – Gasar Firimiya biyar da Gasar Zakarun Turai daya da Kofin FA biyu sai Kofin EFL guda hudu da kuma Community Shields biyu.

A farkon kakar 2022 zuwa 2023 ne Man City ta nada shi matsayin kyaftin bayan dan wasan tsakiyar Brazil Fernandinho ya bar kungiyar kuma zamansa kyaftin ya kawo wa kungiyar gagarumar nasara.

A karshe dai, lamarin ya kare cikin wani sassaukan lissafi daga yadda Man City ke kallon lamarin saboda suna son Gundogan ya ci gaba da zama amma kuma sun girmama matakin da ya dauka na son tafiya.

Guardiola ya yi ta zazzaga wa Gundogan kalmomin yabo musamman a makonnin
karshe na kakar wasannin mai cike da tarihi a kungiyar ta Manchester City sai dai City ba za ta iya kashe ko nawa ba ne, don kawai tana so ta ci gaba da zama da Gundogan.

Zakarun na Ingila da Turai sun yi masa tayin kwanturagin shekara daya da yiwuwar karin kakar wasanni amma Barcelona ta yi masa tayin da ya kunshi karin shekara daya a kan na Manchester City.

Gundogan yana da shekara 32, kuma zakakurin dan wasa a City, yana sane da cewa ‘yan kwallo kafar ne za su iya gasa da shi kuma Man City, a matsayin kungiyar da ta yi nasarar cin kofi uku, suna kan sharafinsu.
‘Yan wasa a yanzu na son zuwa su buga kwallo da Guardiola.

Kungiyar za ta iya samun zaratan ‘yan baiwa, kuma ko Kobacic, yana daf da yin haka sai dai Man City cikin bege za ta rika tunawa da Gundugan tamkar dai David Silva da Yaya Toure da kuma Vincent Kompany.

Gundogan
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

Har Yanzu Ina Da Karfin Buga Wasa A Turai, In Ji Luka Modric

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.