Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce zai ci gaba da ɓata wa masu ƙin Shugaba Bola Tinubu rai ta hanyar aiwatar da ƙarin manyan ayyuka na ci gaba.
Wike ya bayyana haka ne yayin ƙaddamar da sabbin tituna a unguwar Katampe da ke Abuja.
- Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki
- An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC
Titunan sun haɗa da Arterial Road N16 (Shehu Shagari Way) daga Ring Road 1 (Nnamdi Azikiwe Way) zuwa Arterial Road N20 (Wole Soyinka Way).
Shugaba Tinubu da kansa ne ya halarci bikin ƙaddamarwar a ranar Laraba.
A cewar Wike, akwai mutane da ke jin haushi da ci gaban da Tinubu ya kawo tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023.
Ya ce ya fahimci haka ne bayan kallon wani shiri a talabijin inda ya ga wasu mutane na nuna rashin jin daɗi.
Wike ya ce wannan baƙin ciki na su shi ne ke ba shi ƙwarin gwiwa.
“Na ji wani irin abu a zuciyata, sai na kunna talabijin. A nan ne na gano cewa wasu na cikin baƙin ciki saboda abubuwan alheri da ake yi,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa: “Yanzu da na gane suna cikin baƙin ciki, zan ci gaba da sanya musu ƙarin ciwon zuciya. Farin cikinmu na ƙaruwa ne da jin haushinsu. Wannan shi ne sabon aikina na ci gaba da sa musu hawan jini.”
Wike ya yi raha da cewa yayin da suke cikin fushi da damuwa, shi da shugaban ƙasa za su ci gaba da dariya da gudanar da ayyuka.
Ya gode wa Shugaba Tinubu bisa jagorantar abin da ya kira “juyin juya hali na ci gaba.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp