• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ci Gaba Da Yaki Da Cutar Daji Da Matsalolin Mata -Dakta Zainab

by Bushira Nakura
3 years ago
in Adon Gari
0
Zan Ci Gaba Da Yaki Da Cutar Daji Da Matsalolin Mata -Dakta Zainab
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Zainab Shinkafi Bagudu ta yi alkawarin ci gaba da yaki da cutar daji ko da bayan ta bar mulki.

Dakta Zainab dai, wacce kuma ita ce shugabar gidauniyar Medicaid Cancer Foundation ta bayyana hakan a Birnin kebbi a wani taron tattaunawa da ‘yan jarida a wani bangare na kokarin ganin ta samu nasarar gudanar da aikinta daga shekarar 2015 zuwa yau.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Yi Gamsasshen Bayani Game Da “Nord Stream”
  • Matsalar Tsaro Ta Haifar Da Koma-baya A Jihohin Arewa  —Masari

A cewarta, ” cutar daji za ta ci gaba da ta’azzara. Za ta ci gaba da karuwa kuma ana bukatar karin Ma’aikatan da za su gudanar da  aiki don magance matsalar cutar daji.

”Har ila yau, akwai rashin daidaituwa a cikin ayyukan da ake bukata da kuma isassun kudi. Ya kamata a ga ciwon daji a matsayin matsala da za a baiwa muhimmanci da  gaggawa.

“Zan ci gaba da gudanar da ayyukana na tuntubar jama’a don gudanar da yekuwar  da wayar da kan jama’a da ake bukata ta hanyar tattaunawa da masu ruwa da tsaki na jaha da na kasa baki daya.”

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Haka Zalika, Dakta Zainab Bagudu ta ci gaba da cewa, gwamnati da masu ruwa da tsaki a shirye suke su dauki matakin gaggawa domin dakile yaduwar cutar.

Ta yi alkawarin yin aiki tare da gwamnati, kungiyoyi farar hulla da duk masu ruwa da tsaki don kara yawan kudade don yaki da cutar daji, tare da samar da matakan rigakafi.

”Wannan babbar matsala ce a Nijeriya kasancewar kasar ba ta yin abin da ya dace idan aka yi la’akari da yawan al’ummar kasar.

Har ilayau, “Hadin gwiwa mai karfi yana da matukar mahimmanci ta wannan hanyar kamar yadda tsarin tuntubar kasa shima yana da mahimmanci.

Ta ce “Jihar Kebbi ta yi abubuwa da yawa. Muna da tsarin kula da cutar kansa da kuma asusun kansa na marasa galihu.

“Haka kuma akwai tsarin inshorar lafiya musamman a matakin PHC kuma dole ne mu kara himma wajen samar da karin ayyuka,” in ji Dakta Zainab Shinkafi Bagudu.

Ta yi godiya ga maigidanta Gwamna Abubakar Atiku Bagudu   da duk masu ruwa da tsaki bisa yadda aka amince da dokar kare hakkin yara da mata a jihar Kebbi.

Sun hada da dokar BAPP, dokar kare hakkin yara da kuma dokar GBB, inda suka ce matakin da gwamnatin jihar karkashin jagorancin maigidanta Abubakar Atiku Bagudu ta yi abin yabawa ne matuka.

Daga nan ta jaddada bukatar jama’a musamman wadanda aka zalunta da iyayen wadanda aka yi wa fyaden su rika fadin albarkacin bakinsu tare da kai rahoton irin wannan lamari.

”Ya kamata jama’a su dauki matakin da ya dace kuma su samu hujjojin da suka dace. Yakamata kuma a dage da wayar da kan jama’a,” in ji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CututtukaDakta Zainab
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mene Ne Hukuncin Masu Karbar Kudin Dan Siyasa Kuma Su Ki Zabensa?

Next Post

Yadda ‘Yan Nijeriya Ke Shirye-shiryen Shigowar Watan Azumi

Related

tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

2 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

1 month ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

2 months ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

4 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

4 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

7 months ago
Next Post
Yadda ‘Yan Nijeriya Ke Shirye-shiryen Shigowar Watan Azumi

Yadda ‘Yan Nijeriya Ke Shirye-shiryen Shigowar Watan Azumi

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.