• Leadership Hausa
Monday, October 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ci Gaba Da Yaki Da Cutar Daji Da Matsalolin Mata -Dakta Zainab

by Bushira Nakura
7 months ago
in Adon Gari
0
Zan Ci Gaba Da Yaki Da Cutar Daji Da Matsalolin Mata -Dakta Zainab
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Zainab Shinkafi Bagudu ta yi alkawarin ci gaba da yaki da cutar daji ko da bayan ta bar mulki.

Dakta Zainab dai, wacce kuma ita ce shugabar gidauniyar Medicaid Cancer Foundation ta bayyana hakan a Birnin kebbi a wani taron tattaunawa da ‘yan jarida a wani bangare na kokarin ganin ta samu nasarar gudanar da aikinta daga shekarar 2015 zuwa yau.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Yi Gamsasshen Bayani Game Da “Nord Stream”
  • Matsalar Tsaro Ta Haifar Da Koma-baya A Jihohin Arewa  —Masari

A cewarta, ” cutar daji za ta ci gaba da ta’azzara. Za ta ci gaba da karuwa kuma ana bukatar karin Ma’aikatan da za su gudanar da  aiki don magance matsalar cutar daji.

”Har ila yau, akwai rashin daidaituwa a cikin ayyukan da ake bukata da kuma isassun kudi. Ya kamata a ga ciwon daji a matsayin matsala da za a baiwa muhimmanci da  gaggawa.

“Zan ci gaba da gudanar da ayyukana na tuntubar jama’a don gudanar da yekuwar  da wayar da kan jama’a da ake bukata ta hanyar tattaunawa da masu ruwa da tsaki na jaha da na kasa baki daya.”

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Uwana Ne Ke Taya Ni Tallata Kayana – Sumayya Gidado

Ni Mutum Ce Mai Son Na Ga Na Rufa Wa Kaina Asiri – Maryam Nasir

Haka Zalika, Dakta Zainab Bagudu ta ci gaba da cewa, gwamnati da masu ruwa da tsaki a shirye suke su dauki matakin gaggawa domin dakile yaduwar cutar.

Ta yi alkawarin yin aiki tare da gwamnati, kungiyoyi farar hulla da duk masu ruwa da tsaki don kara yawan kudade don yaki da cutar daji, tare da samar da matakan rigakafi.

”Wannan babbar matsala ce a Nijeriya kasancewar kasar ba ta yin abin da ya dace idan aka yi la’akari da yawan al’ummar kasar.

Har ilayau, “Hadin gwiwa mai karfi yana da matukar mahimmanci ta wannan hanyar kamar yadda tsarin tuntubar kasa shima yana da mahimmanci.

Ta ce “Jihar Kebbi ta yi abubuwa da yawa. Muna da tsarin kula da cutar kansa da kuma asusun kansa na marasa galihu.

“Haka kuma akwai tsarin inshorar lafiya musamman a matakin PHC kuma dole ne mu kara himma wajen samar da karin ayyuka,” in ji Dakta Zainab Shinkafi Bagudu.

Ta yi godiya ga maigidanta Gwamna Abubakar Atiku Bagudu   da duk masu ruwa da tsaki bisa yadda aka amince da dokar kare hakkin yara da mata a jihar Kebbi.

Sun hada da dokar BAPP, dokar kare hakkin yara da kuma dokar GBB, inda suka ce matakin da gwamnatin jihar karkashin jagorancin maigidanta Abubakar Atiku Bagudu ta yi abin yabawa ne matuka.

Daga nan ta jaddada bukatar jama’a musamman wadanda aka zalunta da iyayen wadanda aka yi wa fyaden su rika fadin albarkacin bakinsu tare da kai rahoton irin wannan lamari.

”Ya kamata jama’a su dauki matakin da ya dace kuma su samu hujjojin da suka dace. Yakamata kuma a dage da wayar da kan jama’a,” in ji ta.

Tags: CututtukaDakta Zainab
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mene Ne Hukuncin Masu Karbar Kudin Dan Siyasa Kuma Su Ki Zabensa?

Next Post

Yadda ‘Yan Nijeriya Ke Shirye-shiryen Shigowar Watan Azumi

Related

‘Yan Uwana Ne Ke Taya Ni Tallata Kayana – Sumayya Gidado
Adon Gari

‘Yan Uwana Ne Ke Taya Ni Tallata Kayana – Sumayya Gidado

2 days ago
Maryam sani
Adon Gari

Ni Mutum Ce Mai Son Na Ga Na Rufa Wa Kaina Asiri – Maryam Nasir

4 days ago
Tattauna Sirrinki Da Mijinki
Adon Gari

Tattauna Sirrinki Da Mijinki

2 weeks ago
Tunanin Yadda Zan Inganta Rayuwata Ya Sa Na Rungumi Sana’a —Zainab Alhassan
Adon Gari

Tunanin Yadda Zan Inganta Rayuwata Ya Sa Na Rungumi Sana’a —Zainab Alhassan

2 weeks ago
Sana’a Ce Rufin Asirin Mace —Hindatu
Adon Gari

Sana’a Ce Rufin Asirin Mace —Hindatu

4 weeks ago
Mafi Yawan Matan Arewa Ba Sa Samun Horo Da Kwarin Gwiwa – Zainab Ado Bayero
Adon Gari

Mafi Yawan Matan Arewa Ba Sa Samun Horo Da Kwarin Gwiwa – Zainab Ado Bayero

1 month ago
Next Post
Yadda ‘Yan Nijeriya Ke Shirye-shiryen Shigowar Watan Azumi

Yadda ‘Yan Nijeriya Ke Shirye-shiryen Shigowar Watan Azumi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi

October 2, 2023
Mata

Ilimin ‘Ya’ya Mata: Kano Ta Fara Bai Wa ‘Yan Mata 45,000 Tallafin N20, 000

October 2, 2023
Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

Kotu A Amurka Ta Umarci Jami’ar Chicago Ta Bai Wa Atiku Bayanan Karatun Tinubu

October 1, 2023
Tinubu

Ranar ‘Yanci: Tinubu Ya Kara Wa Kananan Ma’aikata N25,000 Kan Albashinsu

October 1, 2023
Hangzhou

Birnin Hangzhou Ya Samu Karuwar Masu Yawon Bude Ido Albarkacin Gasar Wasanni Ta Asiya Dake Gudana

October 1, 2023
Syria

Shugaban Syria: Manyan Tsare-tsare Uku Na duniya Su Ne Jagororin Sabuwar Duniya

October 1, 2023
BUA

Daga Gobe 2 Ga Oktoba Farashin Buhun Simintin BUA Ya Koma N3,500 – Kamfanin

October 1, 2023
Kasar Sin

Ofishin Jakadancin Kasar Sin Dake Najeriya Ya Shirya Bikin Murnar Cikar Sin Shekaru 74 Da Kafuwa

October 1, 2023
Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

Yadda ‘Arewa Peace Ambassador Forum’ Ta Nada Sheikh Muhajjadina Jakadan Zaman Lafiya

October 1, 2023
Amurka

Amurka Ita Ce “Daular Karya”Ta Ko Wace Fuska

October 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.