ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Ci Gaba Da Yaki Da Cutar Daji Da Matsalolin Mata -Dakta Zainab

by Bushira Nakura
3 years ago
Dakta Zainab

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Zainab Shinkafi Bagudu ta yi alkawarin ci gaba da yaki da cutar daji ko da bayan ta bar mulki.

Dakta Zainab dai, wacce kuma ita ce shugabar gidauniyar Medicaid Cancer Foundation ta bayyana hakan a Birnin kebbi a wani taron tattaunawa da ‘yan jarida a wani bangare na kokarin ganin ta samu nasarar gudanar da aikinta daga shekarar 2015 zuwa yau.

  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Yi Gamsasshen Bayani Game Da “Nord Stream”
  • Matsalar Tsaro Ta Haifar Da Koma-baya A Jihohin Arewa  —Masari

A cewarta, ” cutar daji za ta ci gaba da ta’azzara. Za ta ci gaba da karuwa kuma ana bukatar karin Ma’aikatan da za su gudanar da  aiki don magance matsalar cutar daji.

ADVERTISEMENT

”Har ila yau, akwai rashin daidaituwa a cikin ayyukan da ake bukata da kuma isassun kudi. Ya kamata a ga ciwon daji a matsayin matsala da za a baiwa muhimmanci da  gaggawa.

“Zan ci gaba da gudanar da ayyukana na tuntubar jama’a don gudanar da yekuwar  da wayar da kan jama’a da ake bukata ta hanyar tattaunawa da masu ruwa da tsaki na jaha da na kasa baki daya.”

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Haka Zalika, Dakta Zainab Bagudu ta ci gaba da cewa, gwamnati da masu ruwa da tsaki a shirye suke su dauki matakin gaggawa domin dakile yaduwar cutar.

Ta yi alkawarin yin aiki tare da gwamnati, kungiyoyi farar hulla da duk masu ruwa da tsaki don kara yawan kudade don yaki da cutar daji, tare da samar da matakan rigakafi.

”Wannan babbar matsala ce a Nijeriya kasancewar kasar ba ta yin abin da ya dace idan aka yi la’akari da yawan al’ummar kasar.

Har ilayau, “Hadin gwiwa mai karfi yana da matukar mahimmanci ta wannan hanyar kamar yadda tsarin tuntubar kasa shima yana da mahimmanci.

Ta ce “Jihar Kebbi ta yi abubuwa da yawa. Muna da tsarin kula da cutar kansa da kuma asusun kansa na marasa galihu.

“Haka kuma akwai tsarin inshorar lafiya musamman a matakin PHC kuma dole ne mu kara himma wajen samar da karin ayyuka,” in ji Dakta Zainab Shinkafi Bagudu.

Ta yi godiya ga maigidanta Gwamna Abubakar Atiku Bagudu   da duk masu ruwa da tsaki bisa yadda aka amince da dokar kare hakkin yara da mata a jihar Kebbi.

Sun hada da dokar BAPP, dokar kare hakkin yara da kuma dokar GBB, inda suka ce matakin da gwamnatin jihar karkashin jagorancin maigidanta Abubakar Atiku Bagudu ta yi abin yabawa ne matuka.

Daga nan ta jaddada bukatar jama’a musamman wadanda aka zalunta da iyayen wadanda aka yi wa fyaden su rika fadin albarkacin bakinsu tare da kai rahoton irin wannan lamari.

”Ya kamata jama’a su dauki matakin da ya dace kuma su samu hujjojin da suka dace. Yakamata kuma a dage da wayar da kan jama’a,” in ji ta.

Dakta Zainab
Bushira Nakura
+ postsBio
  • Bushira Nakura
    https://hausa.leadership.ng/author/bushira-nakura/
    Butulci Ya Yi Yawa A Siyasar Yanzu – Hon Dankaka
  • Bushira Nakura
    https://hausa.leadership.ng/author/bushira-nakura/
    Ba Ni Da Burin Da Wuce Ziyarar Kabarin Manzon Allah – Fauziyya Sani
  • Bushira Nakura
    https://hausa.leadership.ng/author/bushira-nakura/
    Ba Zan Taba Mantawa Da Zamowata Gwarzuwar Banki Sau Biyu A Jere Ba – Fatima Gana
  • Bushira Nakura
    https://hausa.leadership.ng/author/bushira-nakura/
    Shekara Dayan Abba Ta Fi Takwas Ta Ganduje Albarka – Halima Jalil

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Yadda ‘Yan Nijeriya Ke Shirye-shiryen Shigowar Watan Azumi

Yadda ‘Yan Nijeriya Ke Shirye-shiryen Shigowar Watan Azumi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.