• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Fifita Bangaren Ilimi Idan Na Zama Gwamnan Jihar Kaduna- Sanata Uba Sani

by Ibrahim Ibrahim
3 years ago
uba sani

Dan takarar zama gwamnan jihar Kaduna a jam’iyyar APC, Sanata Uba Sani, ya yi alkawarin ci gaba da ba harkar ilimi fifiko idan har aka zabe shi ya zama gwamna a zabe mai zuwa.

Uba Sani, ya ce, “Gwamnatin PDP ta yi watsi da makarantun gwamnati a cikin shekaru 16 da jam’iyyar ta yi tana mulki, ya yi alkawarin ci gaba daga inda gwamna Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya tsaya, musamman bangaren inganta ilimi, idan ya samu damar zama gwamna.”

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

Sanatan ya bayyana haka ne a wurin taron kaddamar da yakin neman zaben sa a garin Giwa da ke jihar Kaduna a ranar Talata, 17 ga Janairu, 2023.

Dan takarar gwamnan wanda ya ce gwamna El-Rufai ya dawo da martabar da aka rasa a makarantun gwamnati, ya ce: “Abin da na sa a gaba shi ne na samar da ingantaccen ilimi ga ‘yan’uwa talakawa domin hakan ne zai ba su damar samun kyakkyawar makoma da kuma inganta al’umma gaba daya.”

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Haka kuma yi alkawarin karfafa malaman addini tun kafin zaben gwamna na 2023 a jihar, inda ya kara da cewa su na taka muhimmiyar rawa wurin gyara al’umma.

uba sani

Dan takarar gwamnan ya gode wa al’ummar karamar hukumar Giwa bisa goyon bayan gwamnatin APC a matakin tarayya, jiha da kananan hukumomi.

Ya kuma ce, “Ayyukan da aka aiwatar a cikin karamar hukumar Giwa ba za su yiwu ba idan ba tare da tallafin ku ba. Ina so ku ci-gaba da mara wa jamiiyar APC baya ta hanyar zaben jam’iyyar mu a dukkan matakai a zabe mai zuwa,” in ji shi.

Da ya ke jawabi a wurin gangamin, Gwamna Malam Nasir El-Rufai ya bukaci al’ummar Giwa da su zabi Sanata Uba Sani a matsayin magajin sa da kuma Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe a matsayin mataimakiyar sa saboda su na cikin tawagar su ka taimaka wurinn kawo sauyi a jihar Kaduna a karkashin jagoranci na.

Gwamnan ya kuma umarci jama’a da su zabi Muhammad Sani Abdullahi (Dattijo) a matsayin sanata mai wakiltar shiyya ta biyu da Honarabul Bashir Zubairu a matsayin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Giwa da Birnin Gwari.

Ya kuma bukace su da su zabi ‘yan takarar mazabar Giwa ta Gabas da Yamma.

A yayin kamfen din, Mataimakiyar gwamnan ta kaddamar da cibiyar kula da mata masu juna biyu yayin da El-Rufai ya kaddamar da cibiyar wasanni na Unguwa gabanin taron.

Gwamna Nasir El-Rufa’i Sanata Uba Sani, mataimakiyar gwamna Hadiza Sabuwa Balarabe da sauran jami’an gwamnati sun kuma gana da masu ruwa da tsaki, inda suka gabatar da tambayoyi tare da bayyana wasu manufofin gwamnati.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Siyasa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu
Siyasa

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin CBN Na Dakatar Da Karbar Tsofaffin Takardun Naira

Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin CBN Na Dakatar Da Karbar Tsofaffin Takardun Naira

LABARAI MASU NASABA

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.