• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Fifita Bangaren Ilimi Idan Na Zama Gwamnan Jihar Kaduna- Sanata Uba Sani

by Ibrahim Ibrahim
3 years ago
uba sani

Dan takarar zama gwamnan jihar Kaduna a jam’iyyar APC, Sanata Uba Sani, ya yi alkawarin ci gaba da ba harkar ilimi fifiko idan har aka zabe shi ya zama gwamna a zabe mai zuwa.

Uba Sani, ya ce, “Gwamnatin PDP ta yi watsi da makarantun gwamnati a cikin shekaru 16 da jam’iyyar ta yi tana mulki, ya yi alkawarin ci gaba daga inda gwamna Malam Nasir Ahmad El-Rufai ya tsaya, musamman bangaren inganta ilimi, idan ya samu damar zama gwamna.”

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

Sanatan ya bayyana haka ne a wurin taron kaddamar da yakin neman zaben sa a garin Giwa da ke jihar Kaduna a ranar Talata, 17 ga Janairu, 2023.

Dan takarar gwamnan wanda ya ce gwamna El-Rufai ya dawo da martabar da aka rasa a makarantun gwamnati, ya ce: “Abin da na sa a gaba shi ne na samar da ingantaccen ilimi ga ‘yan’uwa talakawa domin hakan ne zai ba su damar samun kyakkyawar makoma da kuma inganta al’umma gaba daya.”

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Haka kuma yi alkawarin karfafa malaman addini tun kafin zaben gwamna na 2023 a jihar, inda ya kara da cewa su na taka muhimmiyar rawa wurin gyara al’umma.

uba sani

Dan takarar gwamnan ya gode wa al’ummar karamar hukumar Giwa bisa goyon bayan gwamnatin APC a matakin tarayya, jiha da kananan hukumomi.

Ya kuma ce, “Ayyukan da aka aiwatar a cikin karamar hukumar Giwa ba za su yiwu ba idan ba tare da tallafin ku ba. Ina so ku ci-gaba da mara wa jamiiyar APC baya ta hanyar zaben jam’iyyar mu a dukkan matakai a zabe mai zuwa,” in ji shi.

Da ya ke jawabi a wurin gangamin, Gwamna Malam Nasir El-Rufai ya bukaci al’ummar Giwa da su zabi Sanata Uba Sani a matsayin magajin sa da kuma Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe a matsayin mataimakiyar sa saboda su na cikin tawagar su ka taimaka wurinn kawo sauyi a jihar Kaduna a karkashin jagoranci na.

Gwamnan ya kuma umarci jama’a da su zabi Muhammad Sani Abdullahi (Dattijo) a matsayin sanata mai wakiltar shiyya ta biyu da Honarabul Bashir Zubairu a matsayin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Giwa da Birnin Gwari.

Ya kuma bukace su da su zabi ‘yan takarar mazabar Giwa ta Gabas da Yamma.

A yayin kamfen din, Mataimakiyar gwamnan ta kaddamar da cibiyar kula da mata masu juna biyu yayin da El-Rufai ya kaddamar da cibiyar wasanni na Unguwa gabanin taron.

Gwamna Nasir El-Rufa’i Sanata Uba Sani, mataimakiyar gwamna Hadiza Sabuwa Balarabe da sauran jami’an gwamnati sun kuma gana da masu ruwa da tsaki, inda suka gabatar da tambayoyi tare da bayyana wasu manufofin gwamnati.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin CBN Na Dakatar Da Karbar Tsofaffin Takardun Naira

Ra’ayoyinku A Kan Wa’adin CBN Na Dakatar Da Karbar Tsofaffin Takardun Naira

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.