• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Gaggauta Rattaba Hannu A Hukuncin Wanda Ya Kone Mutane A Masallaci – Gwamnan Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna yusuf
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa zai yi gaggawar rattaba hannu kan kowanne hukunci kotu ta yanke wa wanda ya kone mutane a garin Larabar Abasawa ana tsaka da sallar Asuba.

Gwamna Abba na wannan bayani ne a loakcin da ya ziyarci asibitin kwararru na Murtala da ke Jihar Kano, inda ya yi Allah wadarai da wannan mummunan abin da matashin ya aikata.

  • Tinubu Ya Miƙa Ta’aziyyarsa Ga Iyalan Waɗanda Suka Ƙone A Gobarar Masallaci A Kano
  • An Fara Shirin Jana’izar Marigayi Raisi A Iran

Ya ce lallai gwamnatinsa ba za ta bar wannan lamari haka ba, inda ya ce wannan hauka ne na karshe kuma rashin imani ne. Ya ce sun sami labarin cewa rigima ce da ta shafi iyali kan rabon gado, amma kuma bai kamata ka rufe kawunnanka da ‘yan’uwanka da sauran al’umma ka banka masu wuta suna sallar Asuba ba.

Gwamnan ya jaddada cewa ko shakka babu a matsayinsa na wadanda Allah ya dora wa nauyin kare lafiya da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano, ba zai taba barin wannan lamari haka ba.

Ya ce, “Na kawo ziyara domin duba wadanda suka samu kuna, wannan abu da wannan mugun mutun ya yi ba shida nasaba da ta’addanci, sannan ba shida nasaba da harkar siyasa, harkace ta cikin gida tsakanin zuriyya guda, an raba gado yana ganin kamar ba a yi masa daidai ba, maimakon bin hanyar doka, shi ne ya yanke wa kansa hukunci ya kashe bayin Allah, saboda shi kafiri ne. Na fada haka ne saboda idan mutun ba kafiri mara imani ba, ba wanda zai je ya tarar da al’ummar Musulmi suna Sallah ya zuba masu fetur ya banka masu wuta.

Labarai Masu Nasaba

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

“Saboda haka ina tabbatar masa da cewa gwamnatina za ta tabbatar da kwato hakkin wadannan mutanen da aka cutar, wadanda suke kwance a wanann wuri da kuma wadanda suka rigamu gidan gaskiya. Sai mun tabbatar da kwato masu hakkinsu, duba da abin da doka ta ce a yi kan wanda ya kashe al’umma.”

Gwamna Abba Kabir ya kuma tabbatar da cewa ba zai jinkirta ba, duk abin da kotun shari’ar Musulunci ta yanke masa, zai rattaba hannu a kai domin tabbatar da cewa yadda suka ji wannan lamarin shi ma ya ji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Dabakona masallata a kanoMasallaci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Za A Zurfafa Dangantakar Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da Kenya

Next Post

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

Related

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

4 minutes ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

4 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

5 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

16 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

17 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

18 hours ago
Next Post
Nijeriya

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

LABARAI MASU NASABA

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.