• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Gaggauta Rattaba Hannu A Hukuncin Wanda Ya Kone Mutane A Masallaci – Gwamnan Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna yusuf
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa zai yi gaggawar rattaba hannu kan kowanne hukunci kotu ta yanke wa wanda ya kone mutane a garin Larabar Abasawa ana tsaka da sallar Asuba.

Gwamna Abba na wannan bayani ne a loakcin da ya ziyarci asibitin kwararru na Murtala da ke Jihar Kano, inda ya yi Allah wadarai da wannan mummunan abin da matashin ya aikata.

  • Tinubu Ya Miƙa Ta’aziyyarsa Ga Iyalan Waɗanda Suka Ƙone A Gobarar Masallaci A Kano
  • An Fara Shirin Jana’izar Marigayi Raisi A Iran

Ya ce lallai gwamnatinsa ba za ta bar wannan lamari haka ba, inda ya ce wannan hauka ne na karshe kuma rashin imani ne. Ya ce sun sami labarin cewa rigima ce da ta shafi iyali kan rabon gado, amma kuma bai kamata ka rufe kawunnanka da ‘yan’uwanka da sauran al’umma ka banka masu wuta suna sallar Asuba ba.

Gwamnan ya jaddada cewa ko shakka babu a matsayinsa na wadanda Allah ya dora wa nauyin kare lafiya da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano, ba zai taba barin wannan lamari haka ba.

Ya ce, “Na kawo ziyara domin duba wadanda suka samu kuna, wannan abu da wannan mugun mutun ya yi ba shida nasaba da ta’addanci, sannan ba shida nasaba da harkar siyasa, harkace ta cikin gida tsakanin zuriyya guda, an raba gado yana ganin kamar ba a yi masa daidai ba, maimakon bin hanyar doka, shi ne ya yanke wa kansa hukunci ya kashe bayin Allah, saboda shi kafiri ne. Na fada haka ne saboda idan mutun ba kafiri mara imani ba, ba wanda zai je ya tarar da al’ummar Musulmi suna Sallah ya zuba masu fetur ya banka masu wuta.

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

“Saboda haka ina tabbatar masa da cewa gwamnatina za ta tabbatar da kwato hakkin wadannan mutanen da aka cutar, wadanda suke kwance a wanann wuri da kuma wadanda suka rigamu gidan gaskiya. Sai mun tabbatar da kwato masu hakkinsu, duba da abin da doka ta ce a yi kan wanda ya kashe al’umma.”

Gwamna Abba Kabir ya kuma tabbatar da cewa ba zai jinkirta ba, duk abin da kotun shari’ar Musulunci ta yanke masa, zai rattaba hannu a kai domin tabbatar da cewa yadda suka ji wannan lamarin shi ma ya ji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Dabakona masallata a kanoMasallaci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Za A Zurfafa Dangantakar Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da Kenya

Next Post

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

9 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

10 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

15 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

17 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

18 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

20 hours ago
Next Post
Nijeriya

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.