• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Gaggauta Rattaba Hannu A Hukuncin Wanda Ya Kone Mutane A Masallaci – Gwamnan Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Gwamna yusuf
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa zai yi gaggawar rattaba hannu kan kowanne hukunci kotu ta yanke wa wanda ya kone mutane a garin Larabar Abasawa ana tsaka da sallar Asuba.

Gwamna Abba na wannan bayani ne a loakcin da ya ziyarci asibitin kwararru na Murtala da ke Jihar Kano, inda ya yi Allah wadarai da wannan mummunan abin da matashin ya aikata.

  • Tinubu Ya Miƙa Ta’aziyyarsa Ga Iyalan Waɗanda Suka Ƙone A Gobarar Masallaci A Kano
  • An Fara Shirin Jana’izar Marigayi Raisi A Iran

Ya ce lallai gwamnatinsa ba za ta bar wannan lamari haka ba, inda ya ce wannan hauka ne na karshe kuma rashin imani ne. Ya ce sun sami labarin cewa rigima ce da ta shafi iyali kan rabon gado, amma kuma bai kamata ka rufe kawunnanka da ‘yan’uwanka da sauran al’umma ka banka masu wuta suna sallar Asuba ba.

Gwamnan ya jaddada cewa ko shakka babu a matsayinsa na wadanda Allah ya dora wa nauyin kare lafiya da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano, ba zai taba barin wannan lamari haka ba.

Ya ce, “Na kawo ziyara domin duba wadanda suka samu kuna, wannan abu da wannan mugun mutun ya yi ba shida nasaba da ta’addanci, sannan ba shida nasaba da harkar siyasa, harkace ta cikin gida tsakanin zuriyya guda, an raba gado yana ganin kamar ba a yi masa daidai ba, maimakon bin hanyar doka, shi ne ya yanke wa kansa hukunci ya kashe bayin Allah, saboda shi kafiri ne. Na fada haka ne saboda idan mutun ba kafiri mara imani ba, ba wanda zai je ya tarar da al’ummar Musulmi suna Sallah ya zuba masu fetur ya banka masu wuta.

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

“Saboda haka ina tabbatar masa da cewa gwamnatina za ta tabbatar da kwato hakkin wadannan mutanen da aka cutar, wadanda suke kwance a wanann wuri da kuma wadanda suka rigamu gidan gaskiya. Sai mun tabbatar da kwato masu hakkinsu, duba da abin da doka ta ce a yi kan wanda ya kashe al’umma.”

Gwamna Abba Kabir ya kuma tabbatar da cewa ba zai jinkirta ba, duk abin da kotun shari’ar Musulunci ta yanke masa, zai rattaba hannu a kai domin tabbatar da cewa yadda suka ji wannan lamarin shi ma ya ji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Dabakona masallata a kanoMasallaci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin: Za A Zurfafa Dangantakar Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da Kenya

Next Post

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

Related

Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

27 minutes ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

1 hour ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

2 hours ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

3 hours ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

4 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

6 hours ago
Next Post
Nijeriya

Dimbin Ma’adinan Kasar Nan Sun Isa Su Kore Mana Talauci -Minista

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.