• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 – Atiku

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
Zan Magance Rashin Aikin Yin Matasa Da Dala Biliyan 10 – Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce zai ware Dala biliyan 10 domin magance matsalar rashin aikin yi a tsakanin matasa idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasar Nijeriya a zaben 2023 mai zuwa.

Atiku ya bayyana hakan ne a Ilorin, babban birnin Jihar Kwara a wajen kaddamar da yakin neman zaben jam’iyyar PDP na Arewa ta Tsakiya, wanda aka gudanar a dandalin Ilorin.

  • Yadda ‘Yan Majalisa Suka Bai Wa Hammata Iska A Saliyo
  • Matsalar Karancin Man Fetur Na Ci Gaba Da Ta’azzara A Legas

Tsohon mataimakin shugaban kasar nan, ya ce za a yi amfani da kudin ne wajen taimaka wa matasan Nijeriya wajen kafa kanana da matsakaitan masana’antu.

“Ina so in tabbatar muku da cewa rashin aikin yi da matasa ke fama da shi a duk fadin kasar nan ba a iya Jihar Kwara ko shiyyar Arewa ta Tsakiya ya tsaya ba, yawancin ku a nan ‘yan kasa da shekara 30 ne kuma yawancin ku a nan ba su da aikin yi ko sana’a. Za mu tabbatar da cewa a cikin shirin namu na yi alkawarin cewa zan ware Dala biliyan 10 don ganin an samar da ayyukan yi ga matasa a kananan da matsakaitan sana’o’i don ba ku dama da kuma tabbatar da cewa an samar muku da ayyukan yi.

“Ba mu zo nan don mu muku karya ba, mu iyayenku ne, muna son ku zama kamar yadda muke, za mu ba ku dama, za mu kawo ku, za mu tabbatar kun cimma burinku, ko mene ne. Babban burin ku, shi ya sa muke nan, kar ku sake zabar APC, ku zabi duk ‘yan takarar PDP a 2023.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

“Mun kuma yi alkawarin dawo da tsaro a duk fadin kasar nan, lokacin da suka zo sai suka ce za su magance matsalar rashin tsaro nan a watanni shida, amma me muke gani? abubuwan da ke faruwa,” in ji Atiku.

Dan takarar shugaban kasar ya bukaci ’yan Kwara da su zabi dukkan ‘yan takarar PDP a zaben 2023 mai zuwa.

Atiku, wanda ya ce a ranar Laraba ne jam’iyyar ta kaddamar da kwamitin mata na PDP, ya kara da cewa ita ce ta farko a tarihin babbar jam’iyyar adawa.

Ya yaba wa al’ummar Jihar Kwara bisa yawan fitowar jama’a tare da gode musu bisa goyon bayan da suka samu da kuma tarbar da tawagar yakin neman zabensa suka yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuKwaraPDPYakin Neman ZabeZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasashen Turai Sun Fusata Da Matakin Amurka

Next Post

An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

9 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

12 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

16 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

19 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

1 day ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

1 day ago
Next Post
An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou

An Bude Bikin Anime Na Kasa Da Kasa Karo Na 18 A Hangzhou

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.