• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zan Yi Aiki A Bayyane Tare Da Shugabannin Majalisa Ta 10 – Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kwana 6 Ga Rantsar Da Tinubu: ‘Yan Jarida Sun Yi Tsokaci Kan Yadda Aka Miƙa Mulki A Gwamnatocin Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Bola Tinubu ya yaba da zaben Godswill Akpabio da Tajudeen Abbas a matsayin shugaban majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai, inda ya tabbatar da cewa zai yi aiki a fili tare da sabbin shugabannin majalisar.

Ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu da kansa a ranar Talata, inda ya bayyana nasarar shugabannin majalisar guda biyu da mataimakansu, Jibril Barau da Benjamin Kalu a matsayin babban ci gaban da aka samu a cikin dimokuradiyyar Nijeriya.

  • An Cafke Mai Sojan Gona A Matsayin Jami’in EFCC Da Sojoji
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Daliban Jami’ar Jos 7

Tinubu ya ce, “A matsayina na shugabanku a shirye nake in yi aiki tare da majalisar dokoki ta kasa a bayyane. ‘Yan Nijeriya na sa ran manyan sanatoci da ‘yan majalisar wakilai za su kafa dokoki da gudanar da ayyukan sa ido da za su inganta ayyukan gwamnati don samun sakamako mai kyau ciki har da inganta rayuwarsu.

“A yayin aikinmu tare, ana iya samun rashin jituwa. Idan ba mu yarda da haka ba, to za mu yaudari kanmu, rashin son zuciya da neman rage wa majalisar dokoki ta kasa ko wani mamba ba zai taba haifar mana da da mai ido ba.”

Shugaban ya tunatar da su cewa, zaben da takwarorinsu suka yi masu a matsayin shugabanni da kuma dora ragamar shugabancin majalisar babban abin alfahari ne da ke tattare da gagarumin nauyi tare da fatan za su ba da marasa kunya wajen aiki kafada da kafada da sauran ‘yan majalisa da kuma daukacin ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Ya jajanta wa Abdulaziz Yari da Idris Wase da kuma Aminu Jaji wadanda suka fadi zabe bisa inganta tsarin shugabanni majalisa ta 10. Ya yi kira gare su da su ci gaba da gajircewa kamar yadda suka yi a takarar shugabancin majalisar dokokin kasa wajen gudanar da ayyukansu ga al’ummar mazabarsu da kuma  Nijeriya.

Tinubu ya taya daukacin ‘yan majalisar dokoki ta kasa wadanda a suka shiga aikin yi wa al’ummar kasar nan hidima.

Ya gargade su da cewa, “Muna yin kira ga dukkaninmu mu yi kokarin sauke nauyin da ke kanmu da kuma amfani da rantsuwar da muka yi na hakkin hidimta wa kasarmu. Lokaci ya yi da za mu ci gaba da tafiya tare wajen gudanar da harkokin mulki domin ci gaban Nijeriya.

 “Mutane a fadin kasar nan suna sa rai sosai daga gare mu. Suna son mu sauke nauyinsu na tattalin arziki. Suna son mu kawar da rashin tsaro domin manomanmu na karkara su je gonakinsu su noma abincin da muke ci.”

“Mutanenmu sun zuba mana ido mu gyara arzikin kasarmu da kuma kawar da duk wani shingen da ke hana ci gaba. Duk wadannan za mu iya yi ne kadai idan muka jajirce. Za mu iya cimma dukkan kyawawan abubuwan da muka alkawarta a lokacin yakin neman zabe idan muka yi aiki tare cikin jituwa da mutunta hakkinmu da kuma maslahar kasarmu.

“Ba za mu yi watsi da wannan damar ba saboda ‘yan Nijeriya suna son mu yi amfani da kowace rana a cikin shekaru hudu masu zuwa. A bisa lamarin gaskiya, mutanenmu suna son mu rubayya kokarin gwamnatinmu. Hakika sun cancanci shugabanci nagari mai cike da adalci wanda zai inganta rayuwarsu. Dole ne mu ba su iya abin da zamu iya.

“Zan ci gaba da abokin kowa don samun zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaban Nijeriya. Ina kira ga shugabannin majalisar dokoki ta kasa ta 10 da dukkan ‘yan majalisa su yi aiki tare da ni a wannan tafiya ta gwamnati.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikimajalisaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnonin Arewa Maso Yamma Sun Gana Da Tinubu Kan Matsalar Tsaro

Next Post

Idan Ruwan Dagwalon Nukiliya Bai Gurbata Ba, Me Yasa Japan Ba Ta Ajiye Shi Ba?

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Idan Ruwan Dagwalon Nukiliya Bai Gurbata Ba, Me Yasa Japan Ba Ta Ajiye Shi Ba?

Idan Ruwan Dagwalon Nukiliya Bai Gurbata Ba, Me Yasa Japan Ba Ta Ajiye Shi Ba?

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.