• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kisan Kai: Zargin Da Ake Wa Doguwa Ya Saba Da Kundin Tsarin Mulki – Kotu

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Doguwa

Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a jihar Kano ta ayyana cewa zargin kisan kai da hada kai wajen yin kisa da ake yi wa shugaban masu rinjaye na Majalisar wakilai, Alhassan Ado Doguwa ya saba wa kundin tsarin mulkin kasa.

Da yake jagorantar hukunci kan bukatar da Doguwa ya shigar kan tauye masa hakki da ‘yanci da tsare shi ba bisa ka’ida ba da karamar kotu ta yi, Mai Shari’a Mohammed Yunusa, a ranar Litinin ya ce, babban Kotun Majistire ba ta da hurumin sauraron karar da ya shafi aikata manyan laifuka.

  • Ba Ni Da Hurumin Gurfanar Da Alhassan Doguwa —Antoni-Janar
  • Alhassan Ado Doguwa Ya Sake Lashe Zaben Dan Majalisar Wakilai A Kano

Mai Shari’a Yunusa ya buga misali da sashi na 251 (1) da ya ce babbar Kotun tarayya ce kadai ke da ikon sauraron karar da ta shafi bindigu kamar dai irin tuhumar da aka shigar kan Ado Doguwa.

Sai dai Alkalin ya nanata cewa ba fa kawai don an amince da bada belin Doguwa shi ke nan hakan na nuni da cewa ya samu kariyar da ba zai fuskanci shari’a ba ne, Yunusa ya ce dole a bi komai bisa doka da ka’ida.

Lauyan Ado Doguwa, Nureini Jimoh, shi ne ya nema masa umarnin samun kariya kan ‘yancin dan adamtaka kamar yadda dokar kasa ta bayar da dama ga kowa.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

Lauyan nasa ya yi ikirarin cewa ‘yansanda sun tsare Doguwa ba bisa ka’ida ba wanda hakan ya taba masa hakkinsa da ‘yancinsa kamar yadda dokokin mulkin kasa na 1999 suka bayar.

Kazalika, ya bukaci kotun ta ayyana cewar sauraron karar da kotun Majistire ta yi bai dacewa ba kuma ajingine shi tare da ayyana cewar hakan ya saba wa tsarin mulkin kasa domin ba ta da hurumin da karfin ikon sauraron irin wannan karar da suka shafi manyan laifuka.

Alkali Yunusa ya ce ‘yan kasa na da dama bisa tanade-tanaden doka sashi na 46 (1) na kundin tsarin mulkin kasa ta 1999 da su je kowace babban kotu domin kalubalantar yunkurin tauye musu hakkinsu.

Mai Shari’a Yunusa ya ce tun da farko ma Bai dace a tsare Doguwa a gidan yari ba domin ba a gabatar da karar da ake masa ta hanyoyin da suka dace ba, ya kara da cewa shigar da karar da ‘yan sanda suka yi a karamar kotu bai dace ba.

Don haka ne ya haramta wa ‘yansanda kamawa, musgunawa ko tsare Alhassan Doguwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC
Labarai

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 
Labarai

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Next Post
NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.