• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

’Yan Nijeriya biyu Collins da Osas, an ruwaito sun rasu a birnin Tripoli, babban birnin kasar Libya, mutuwar da ake zargin tana da alaka cin guba, kamar yadda PUNCH Metro ta wallafa. Wakilinmu ya nakalto a ranar Asabar, cewa wadanda abin ya shafa, wadanda duk suna zaune a yankin Misrata ta kasar, sun yi tafiya zuwa Tripoli a ranar 20 ga Yuli tare da wani aboki da ba a bayyana sunansa ba.

“Wata majiya daga dangin marigayi Collins, ta shaida wa PUNCH Metro cewa a ranar Asabar cewa an ce abokin ya bar su a can ya koma Misrata shi kadai, daga baya ya samu kiran waya cewa abokan tafiyarsa biyun sun rasu bayan zargin an basu guba.”

  • Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina
  • Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

“An shaida mana cewa su uku suna zaune a Misrata, sannan dukkansu suka yi tafiya zuwa wani wuri da ake kira Oshofana a Tripoli domin shakatawa. Ko da yake Collins da Osas ba su saba da wurin ba, shi ne karo na farko da suka je can. An ce wuri ne da ake gudanar da kasuwanci iri-iri.”

“Don haka, bayan sun kwana hudu a can, abokin da suka bi zuwa wurin ya ce zai koma Misrata, amma Collins da Osas suka ce za su ci gaba da zama a wurin. Sai ya bar su a wurin ya koma. Bayan kusan kwanaki biyu ne ya ce ya samu kiran waya cewa abokan aikinsa biyun sun rasu ana zargin guba aka basu a abinci,” in ji majiyar.

“Wata majiya cikin kasar ta shaida wa wakilinmu cewa lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce tun tuni.”

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Labarin abokinsu da ya bayar bayan ya dawo gida ya haifar da zargi.

“A sanin da muka yio wa Oshofana, labarin mutumin da suka bi zuwa wurin dole ya haifar da zargi. Wannan shi ne abin da ya gaya mana domin babu wanda ya tafi tare da su. Amma wasu daga cikin abokan aikimu nan ba su gamsu da bayaninsa ba, suna kuma bin diddigin binciken da ake yi domin gano musabbabin mutuwarsu,” in ji majiyar.”

Majiyar ta kara da cewa an riga an binne abokan da suka rasu a cikin kasar.

Da aka tuntubi mai magana da yawun Hukumar ‘Yan Nijeriya mazauna kasashen waje, Abdulrahman Balogun, ya ce bai da masaniya kan lamarin.

Ya ce, ‘Ban san da lamarin ba, amma iyalansu na iya rubuta korafi zuwa gare mu a matsayin hukuma, kuma za mu yi aiki a kai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Guba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Next Post

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Related

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

1 month ago
Next Post
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

LABARAI MASU NASABA

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.