• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Tarkon Bashi Na Shan Suka Daga Sassan Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Tarkon Bashi Na Shan Suka Daga Sassan Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar kafafen watsa labaran yammacin duniya, da irin kalaman da kan fito daga bakunan manyan jamian Amurka, ba zai rasa jin zarge-zarge marasa dalili kan kasar Sin ba. Cikin wadanda suka fi fitowa fili, a baya bayan nan an ji zargin cewa wai kasar Sin na Danawa kasashen Afirka Tarkon Bashi. Kana a baya bayan nan ma, an jiyo sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen, na cewa wai Sin ta yiwa shirin tattaunawa game da lamunin da kasar Zambia ke karba kafar ungulu.

Idan muka bibiyi wannan kalamai na Janet Yellen, za mu ga ba su da tushe ko kadan, domin kuma su kansu mahukuntan kasar Zambia sun musanta hakan, suna masu bayyana kalaman da cewa sam ba su dace su fito daga bakin babbar jamiar Amurka ba. Har ma wasu masu fashin baki na cewa bai dace jamiar ta furta kalamai masu nasaba da alakar Sin da Zambia, yayin da take ziyarar aiki a Zambia ba, domin da farko ma hakan ya sabawa daar ayyukan diflomasiyya.

  • Xi Jinping Ya Gabatar Da Sakon Bidiyo Ga Taron Koli Karo Na 7 Na Kungiyar Kasashen Latin Amurka Da Caribbean

Kaza lika, matsayar Sin game da bashin dake tsakaninta da Zambia a bayyane take, kasancewar Sin da Zambia kawaye ne na tsawon lokaci, kuma abokan hadin gwiwar samar da ci gaba. Ana iya shaida hakan, idan aka dubi yadda Sin ta tallafawa Zambia da kudaden gudanar da layin dogo da ya hada Tanzania da Zambia tun a shekarun 1970, lokacin da ita kanta Sin ba ta da cikakkiyar wadata.

Har ila yau a yanzu ma, Sin ta samar da kudaden aiwatar da manyan ayyukan raya kasa a Zambia, wanda hakan ke dada tabbatar da aniyarta ta ingiza ci gaban kasar.

Ko shakka babu, kalaman waccan jamia ta Amurka sun sabawa kaida, kuma akwai bukatar tsagin Amurka ya yi amfani da damarsa, ta inganta alaka da Zambia wajen gabatar da agaji na kara bunkasa kasar, maimakon mayar da Sin abun suka a idon sahihan kawayen ta na nahiyar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Wasu dai na kallon irin wadannan kalamai daga jamian Amurka, a matsayin kunna wutar yakin cacar baka, da nuna alamu na wata mummunar takara tsakanin ta da sauran kasashen duniya dake kawance da kasashen Afirka. Har ma wasu na cewa, idan har Amurka ba ta sauya matsa wajen kallon Sin a matsayin wata barazana ba, hakan na iya zama manuniya dake tabbatar da cewa, burin Amurka shi ne mayar da nahiyar Afirka fagen dagar takara, maimakon wuri da za a tallafawa ya samu ci gaban da yake fata, kuma nahiya da ke bukatar hadin kan dukkanin kasashen da suka ci gaba, ta yadda za a gudu tare a tsira tare! (Saminu Hassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Kan Rashin Kulawa

Next Post

Ku Daina Bin Layin Bankuna, Ku Cire Kudi A Wajen Masu POS – CBN Ga Kwastomomi

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

13 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

14 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

16 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

16 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

18 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

20 hours ago
Next Post
Ku Daina Bin Layin Bankuna, Ku Cire Kudi A Wajen Masu POS – CBN Ga Kwastomomi

Ku Daina Bin Layin Bankuna, Ku Cire Kudi A Wajen Masu POS - CBN Ga Kwastomomi

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.