• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Zartar Da Hukuncin Kisa Ya Karu A Duniya, In Ji Amnesty
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yawan aiwatar da hukuncin kisa ya karu a duniya kamar yadda alkaluman da hukumar kare hakkin dan’adam ta duniya ta Amnesty International ta fitar suka nuna.

Kungiyar ta samu alkaluma 1,153 na kisan a 2023, karin kashi 31 cikin dari daga kisa 883 da aka tabbatar sun wanzu a 2022.

  • DSS Sun Cafke Dan Jarida A Filin Jirgin Sama Akan Hanyarsa Ta Zuwa Umrah Daga Kano
  • Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Wadannan su ne alkaluma mafiya girma da kungiyar ta Amnesty International ta tattara tun 2015, lokacin da aka aiwatar da hukuncin kisa kan mutum 1,634.

Babbar Sakatariyar kungiyar ta Amnesty Agnès Callamard ta bayyana cewa tashin gwauron zabi da aka samu na yawan aiwatar da hukuncin kisan yawanci ya kasance ne a Iran.

Ta ce hukumomin Iran suna nuna rashin mutunta rayuwar dan’adam, inda suke aiwatar da hukuncin kisa hatta a kan laifukan da suke da alaka da miyagun kwayoyi, tana mai karin bayani da cewa wannan na nuni da yadda hukumomin Iran ke nuna wariya ga al’ummar kasar mai rauni.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

Duk da cewa rahoton ya nuna cewa Iran ta aiwatar da yawancin hukuncin kisan kan akalla mutum 853, Amnesty na ganin cewa China ce ta fi aiwatar da hukuncin kisa a duniya.

Duk da cewa babu wasu alkaluma da China ta fitar na aiwatar da hukuncin kisa to amma kiyasin Amnesty ya nuna dubban mutane aka kashe a kasar a shekarar da ta wuce.

Amnesty ta kuma lura cewa hukuncin kisa da aka yanke a duniya ya karu da kashi 20 cikin dari a 2023.

Wannan shi ne hukuncin kisa mafi yawa da aka yanke tun 2018.

Wadanne kasashe ne suka fi aiwatar da hukuncin kisa?

Amnesty ta ce kasashe biyar da suka fi aiwatar da hukuncin kisa a 2023 su ne, China, da Iran, da Saudiyya, da Somalia da kuma Amurka.

Iran kadai tana da kashi 74 cikin dari, yayin da Saudi Arabia take da kashi 15 cikin dari.

To amma a kan China, Amnesty, ta ce ba ta da alkaluma da hukumomi suka fitar, kamar yadda ba ta da su daga Koriya ta Arewa da Bietnam, da Syria, da Yankin Falsdinawa da kuma Afghanistan.

Kasashe nawa ne suka soke aiwatar da hukuncin kisa?

Yawan kasashen da suka soke hukuncin kisa ya karu daga 48 a1991 zuwa 112 a 2023.

Kasashe tara sun aiwatar da hukuncin a kan manyan laifuka, yayin da kasashe 23 da suke da dokar ba su aiwatar da hukuncin ba a cikin akalla shekara 10.

Ta yaya kasashen duniya ke aiwatar da hukuncin kisan?

Akwai hanyoyi hudu mafiya shahara wadanda ake bi wajen aiwatar da hukuncin a 2023, inda Saudiyya ce kadai ke fille kai.

Kasashe bakwai suna amfani da rataya, shida ta hanyar harbi, yayin da uku suka yi amfani da allurar guba a bara.

Babban Jami’in Majalisar Duniya Mai Kula da Kare Hakkin Dan’adam Bolker Türk ya ce, abu ne mai wuya a iya danganta aiwatar da hukuncin kisa da mutunta dan’adam, da ‘yancin rayuwa na mutum, da yin rayuwar da ba ta da azabtarwa ko gana akuba ko kaskantarwa ko kuma hukunta mutum.

Wanke mutum daga laifi

Wanke mutum, shi ne bayan an yanke masa hukuncin kisa, ya daukaka kara kuma bai yi nasara ba, yayin da yake zaman jiran aiwatar da hukuncin, sai daga baya a wanke shi daga laifin a kuma sallame shi da cewa ba shi da laifi a hukumance.

Amnesty International ta samu irin wannan har guda tara a kasashe uku inda aka wanke fursunonin da aka yanke wa hukuncin kisa amma daga baya aka wanke su. Kasashen su ne : Kenya (mutum 5), Amurka (mutum 3), Zimbabwe (mutum1).

Masu rajin kare hakkin dan’adam na yaki da yanke wa mutane hukuncin kisa, domin nuna aibun yanayin da ake samu na wanke mutum bayan an riga an aiwatar da hukuncin wato an kashe mutum.

Hukuncin kisa domin zama darasi

Ofishin kare hakkin dan’adam na Majalisar Dinkin Duniya ya ce, kasashe suna yin hukuncin kisa ne domin ya zama darasi- wato hana mutane aikata laifi.

Abin da yawancin masana kimiyyar halayyar dan’adam suka yi amanna da shi shi ne cewa yarda da cewa hukuncin kisa na hana aikata laifi, babu shaida da ta tabbatar da haka a cewar masanan.

Wasu sun ce abin da ke hana yawanci aikata laifi shi ne yuwuwar kama mutum da kuma hukunta shi.

A shekara ta 1988 an gudanar da wani bincike ga Majalisar dinkin duniya domin gano alakar hukuncin kisa da yawan kisan kai. An kuma sabunta wannan a 1996. Daga nan ne aka amince da cewa bincike ya kasa tabbatar da shaida ta kimiyya cewa hukuncin kisa ya fi tasiri a kan daurin rai da rai.

Tasirin hukunci kisa a zukatan yara

A 2010, kasashe14, da suka hada da Algeria, da Argentina, da Kazakhstan, da Medico da kuma Turkiyya, sun hadu suka kafa wata hukuma da ke yaki da hukuncin kisa.

Hukumar ta kara fadada zuwa kasashe 24 da suka hada da Birtaniya da Kanada da Australia, da Jamus da Togo.

A cikin rahoton da ta fitar a baya-bayan nan, hukumar ta jaddada cewa, yara na fuskantar barazanar kisa a kasashe da dama, duk da yarjejeniyar da Majalisar Dinkin Duniya kan hakkin yara, ta haramta yin hakan. Yarjejeniyar na aiki a kasashe 196.

Kungiyar Kwararrun Masana Halayyar Dan’adam (APA) ta yi kira ga jihohin Amurka su haramta aiwatar da hukuncin kisa ga duk dan kasa da shekara 21.

APA ta rubuta cewa: “Bisa ga yanayin kimiyya da ake ciki a yanzu, ba za a iya cewa kwakwalwar ’yan shekara 18 zuwa 20 ta bambanta da na ’yan shekara 17 ba.”

Ta ci gaba da cewa: “Halayen kuruciyar matasa na tabbatar da rashin zartar da hukuncin kisa a kan yara masu shekaru 16 da 17 suna cikin ’yan shekara 18 zuwa 20.”

Ba kawai yara abin ya shafa ta hanyar kisa ba. “Ba kamar sauran nau’in hukunce-hukuncen laifuka ba, zartar da hukuncin kisa ga iyaye na dadewa a zukatan yara,” in ji Hukumar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmnestyCourtHangingkillingMurderPolice
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gudunmawa 10 Da Ilimi Ke Bayarwa Ga Al’umma (2)

Next Post

Ina So Na Ga Ina Kyautata Wa Iyayena Har Ma Da Bare

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

1 month ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Ina So Na Ga Ina Kyautata Wa Iyayena Har Ma Da Bare

Ina So Na Ga Ina Kyautata Wa Iyayena Har Ma Da Bare

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.