ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina So Na Ga Ina Kyautata Wa Iyayena Har Ma Da Bare

by Maryam Auyo
2 years ago
Iyaye

Maryam Abdullahi matashiya ce da ta yi karatun Boko mai zurfi, amma duk da haka ba ta tsaya neman aikin gwamnati ba ta tsunduma harkar kasuwanci, wanda kuma take samu tagomashi a kasuwancin nata.

Ta tattauna da wakiliyarmu BIKISU TIJJANI KASSIM a kan yadda take gudanar da harkokinta wanda a karkashinsa ta ce tana so ta ga tana kyautata wa iyaye har ma da bare da ba su hada komai da ita ba. Bugu da kari ta nusar da mata cewa su sani fa darajar ‘ya mace ita ce kan gaba da komai, don haka mata su kare mutuncinsu. Ga dai yadda ta kasance a tsakaninsu:

  • Gwamnan Jigawa Umar Namadi Ya Raba Kayan Makaranta 30,000 Ga Dalibai Mata
  • Gwamnatin Kano Ta Biyawa Ɗalibai 119,903 Kudin Jarrabawar NECO Da NBAIS

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

ADVERTISEMENT

Suna na Maryam Abdullahi Auyo, ni ‘yar asalin Auyo ce a Jihar jigawa. Na yi firamare a Jihar kano, na yi sakandire a Jihar jigawa na yi jami’a a Jihar Kano.

 

LABARAI MASU NASABA

Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

GORON JUMA’A

Shin Maryam matar aure ce?

A’a ba ni da aure

Malama Maryam ‘yar kasuwa ce ko kuma ma’aikaciya ce?

Ni ‘yar kasuwa ce

Wanne irin kasuwanci kike yi?

Ina kasuwancin Online na ‘General Merchandise sunan Kamfanina Auyo’s Enterprise. Ina nan a Facebook, Instagram da sunan Auyo’s Enterprise da kuma Whatsapp.

Shin me kasuwancin naki ya kunsa, ma’ana kamar me da me kike sarrafawa?

Ina sayar da kayan sakawa, kimar su; Atamfa, Laces, Shadda, Yards, Abaya, Jallabiya, Hijabai, Kayan Bacci, Gyale, Sarka, Takalma, Kayan Kicin, Zanin Gado, Labulaye da dukkan abubuwan bukata, kuma har kayan aure ina hadawa.

Me ya ja hankalinki har kika shiga wannan kasuwancin?

Babban burin kowa rufin asiri, ina so na ga ina iya kyautatawa iyayena da ‘yan uwa na, har ma bare, Allah ya raba mu da haram Amin.

Maryam ba ki fada mana matakin karatunki ba?

Ina da BSc Education Chemistry

Wane irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

aminci shi ne komai a kasuwancin online, idan na hadu da wanda ba ya yarda da mutane saboda yanayin zamani shi ne nake fuskantar kalubale.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika cimma?

Alhamdulillah, cikin ikon Allah kasuwancina ya karbu ina kuma ganin ci gaba ta hanyoyi da dama, hakan babbar nasara ce a wajena.

Maryam Abdullah Auyo
Maryam Abdullah Auyo

Wane abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Na ga an sayi kayana, kuma kaya sun je hannun mai saye ba tare da an samu matsala ba sai ma yabawa da ya yi.

Dame kike so mutane su rika tunawa da ke?

Da alkhairi nake so a dinga tunawa da ni.

Ga karatu, ga kuma hidimomin sana’a, shin ta yaya kike samun damar gudanar da hutunki?

Ina hutawa a duk lokacin da na samu, lokacin da ban samu ba kuma, ba komai haka zan shiga harkokina, lafiya itace gaba.

Wacce irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Idan aka nemar min Aljannah da Albarka a wajen Allah.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Suna bani goyon baya dari bisa dari, ga dukkan abubuwan da nake sawa gaba sai dai Allah ya saka musu da alkhairi Amin.

Kawaye fa?

Kawayena mutanan kirki ne suma dukkan goyan baya ina samu a wajensu gaskiya, sai dai na ce Allah ya saka musu da alkhairi.

Me kike fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Atamfa karshen adon Bahaushiya, kayan kwalliya kuma agogo.

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Darajar ‘ya mace tana gaba da komai, ya kamata mu kiyaye kanmu daga tozarci da wulakanci, mu kare mutuncinmu. Mu kuma ci gaba da addu’o’i.

Ban hakuri:

Muna bai wa masu karatu hakuri saboda kuskuren da aka samu a wannan shafi a makon da ya gabata, na hada hoton Maryam da wata tattaunawar da ba tata ba.

Don haka muka gyara muka sake wallafa tattaunawar.

Mun gode!

Edita

Iyaye
Maryam Auyo
+ postsBio

    MASU ALAKA

    Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
    Tattaunawa

    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello

    July 11, 2026
    GORON JUMA’A
    Madubin Rayuwa

    GORON JUMA’A

    June 12, 2026
    GORON JUMA’A
    Madubin Rayuwa

    GORON JUMA’A

    May 1, 2026
    Next Post
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

    Majalisar Dinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

    LABARAI MASU NASABA

    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

    July 15, 2026
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

    July 15, 2026
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

    July 15, 2026
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

    July 15, 2026
    Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

    Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

    July 15, 2026
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

    July 15, 2026
    Sabbin Ministoci

    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

    July 15, 2026
    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

    GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

    July 15, 2026
    ‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

    Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

    July 15, 2026
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

    July 15, 2026

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

    No Result
    View All Result
    • Gida
    • Labarai
      • Manyan Labarai
      • Kananan Labarai
      • Masarautu
      • Bakon Marubuci
      • Dausayin Musulunci
      • Daga Kasar Sin
      • Nishadi
      • Noma Da Kiwo
      • Sana’a Sa’a
      • Tambarin Dimokuradiyya
      • Taskira
      • Daga Birnin Sin
      • Ado Da Kwalliya
    • Siyasa
    • Wasanni
    • Al’adu
    • Al’ajabi
    • Labaran Kasuwanci
    • Karanta cikin Turanci

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.