ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ina So Na Ga Ina Kyautata Wa Iyayena Har Ma Da Bare

by Maryam Auyo
2 years ago
Iyaye

Maryam Abdullahi matashiya ce da ta yi karatun Boko mai zurfi, amma duk da haka ba ta tsaya neman aikin gwamnati ba ta tsunduma harkar kasuwanci, wanda kuma take samu tagomashi a kasuwancin nata.

Ta tattauna da wakiliyarmu BIKISU TIJJANI KASSIM a kan yadda take gudanar da harkokinta wanda a karkashinsa ta ce tana so ta ga tana kyautata wa iyaye har ma da bare da ba su hada komai da ita ba. Bugu da kari ta nusar da mata cewa su sani fa darajar ‘ya mace ita ce kan gaba da komai, don haka mata su kare mutuncinsu. Ga dai yadda ta kasance a tsakaninsu:

  • Gwamnan Jigawa Umar Namadi Ya Raba Kayan Makaranta 30,000 Ga Dalibai Mata
  • Gwamnatin Kano Ta Biyawa Ɗalibai 119,903 Kudin Jarrabawar NECO Da NBAIS

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

ADVERTISEMENT

Suna na Maryam Abdullahi Auyo, ni ‘yar asalin Auyo ce a Jihar jigawa. Na yi firamare a Jihar kano, na yi sakandire a Jihar jigawa na yi jami’a a Jihar Kano.

 

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

Shin Maryam matar aure ce?

A’a ba ni da aure

Malama Maryam ‘yar kasuwa ce ko kuma ma’aikaciya ce?

Ni ‘yar kasuwa ce

Wanne irin kasuwanci kike yi?

Ina kasuwancin Online na ‘General Merchandise sunan Kamfanina Auyo’s Enterprise. Ina nan a Facebook, Instagram da sunan Auyo’s Enterprise da kuma Whatsapp.

Shin me kasuwancin naki ya kunsa, ma’ana kamar me da me kike sarrafawa?

Ina sayar da kayan sakawa, kimar su; Atamfa, Laces, Shadda, Yards, Abaya, Jallabiya, Hijabai, Kayan Bacci, Gyale, Sarka, Takalma, Kayan Kicin, Zanin Gado, Labulaye da dukkan abubuwan bukata, kuma har kayan aure ina hadawa.

Me ya ja hankalinki har kika shiga wannan kasuwancin?

Babban burin kowa rufin asiri, ina so na ga ina iya kyautatawa iyayena da ‘yan uwa na, har ma bare, Allah ya raba mu da haram Amin.

Maryam ba ki fada mana matakin karatunki ba?

Ina da BSc Education Chemistry

Wane irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

aminci shi ne komai a kasuwancin online, idan na hadu da wanda ba ya yarda da mutane saboda yanayin zamani shi ne nake fuskantar kalubale.

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika cimma?

Alhamdulillah, cikin ikon Allah kasuwancina ya karbu ina kuma ganin ci gaba ta hanyoyi da dama, hakan babbar nasara ce a wajena.

Maryam Abdullah Auyo
Maryam Abdullah Auyo

Wane abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Na ga an sayi kayana, kuma kaya sun je hannun mai saye ba tare da an samu matsala ba sai ma yabawa da ya yi.

Dame kike so mutane su rika tunawa da ke?

Da alkhairi nake so a dinga tunawa da ni.

Ga karatu, ga kuma hidimomin sana’a, shin ta yaya kike samun damar gudanar da hutunki?

Ina hutawa a duk lokacin da na samu, lokacin da ban samu ba kuma, ba komai haka zan shiga harkokina, lafiya itace gaba.

Wacce irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Idan aka nemar min Aljannah da Albarka a wajen Allah.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Suna bani goyon baya dari bisa dari, ga dukkan abubuwan da nake sawa gaba sai dai Allah ya saka musu da alkhairi Amin.

Kawaye fa?

Kawayena mutanan kirki ne suma dukkan goyan baya ina samu a wajensu gaskiya, sai dai na ce Allah ya saka musu da alkhairi.

Me kike fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Atamfa karshen adon Bahaushiya, kayan kwalliya kuma agogo.

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Darajar ‘ya mace tana gaba da komai, ya kamata mu kiyaye kanmu daga tozarci da wulakanci, mu kare mutuncinmu. Mu kuma ci gaba da addu’o’i.

Ban hakuri:

Muna bai wa masu karatu hakuri saboda kuskuren da aka samu a wannan shafi a makon da ya gabata, na hada hoton Maryam da wata tattaunawar da ba tata ba.

Don haka muka gyara muka sake wallafa tattaunawar.

Mun gode!

Edita

Iyaye
Maryam Auyo
+ postsBio

    MASU ALAKA

    GORON JUMA’A
    Madubin Rayuwa

    GORON JUMA’A

    May 1, 2026
    Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu
    Tattaunawa

    Har Yanzu Ana Yin Allah-wadai Da Cin Amanar Da Aka Yi Wa Kwankwaso – Hon. MB Aliyu

    April 10, 2026
     Saraki Zai Jagoranci Kwamitin Gyara Jam’iyyar PDP 
    Tattaunawa

    Dalilin Da Ya Sa PDP Ke Cikin Rikici, Za Ta Dawo Da Karfin Ta —Saraki

    April 4, 2026
    Next Post
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

    Majalisar Dinkin Duniya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

    LABARAI MASU NASABA

    Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

    June 4, 2026
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

    June 4, 2026
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

    June 4, 2026
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

    June 4, 2026
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

    June 3, 2026
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

    June 3, 2026
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

    June 3, 2026
    Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

    June 3, 2026
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

    June 3, 2026
    Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

    Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

    June 3, 2026

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

    No Result
    View All Result
    • Gida
    • Labarai
      • Manyan Labarai
      • Kananan Labarai
      • Masarautu
      • Bakon Marubuci
      • Dausayin Musulunci
      • Daga Kasar Sin
      • Nishadi
      • Noma Da Kiwo
      • Sana’a Sa’a
      • Tambarin Dimokuradiyya
      • Taskira
      • Daga Birnin Sin
      • Ado Da Kwalliya
    • Siyasa
    • Wasanni
    • Al’adu
    • Al’ajabi
    • Labaran Kasuwanci
    • Karanta cikin Turanci

    © 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.