• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ziri Daya Da Hanya Daya” Da Ke Haifar Da Alfanu Ga Al’ummar Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Al'ummar duniya

A kwanakin baya ne, aka kammala kashi na farko na layin dogo mai amfani da lantarki a jihar Lagos, tarayyar Nijeriya, wanda ke zama irinta ta farko a yammacin Afirka, haka kuma karin nasara da aka cimma a kokarin aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, ko kuma “Belt and Road Initiative” a Turance. Da yake kaddamar da aikin, gwamnan jihar Lagos Babajide Olusola Sanwo-Olu, ya bayyana shi a matsayin wanda zai saukaka matsalar zirga-zirga da ake fuskanta a jihar, kana abin koyi ga Nijeriya da ma sauran kasashen yammacin Afirka wajen shimfida layukan dogo.

A cikin shekarar da ta gabata, an aiwatar da hadin gwiwar “ziri daya da hanya daya” tare da dimbin nasarori, inda a cikin watanni 11 na farkon shekarar, jimillar kudin ciniki a tsakanin kasar Sin da sauran abokananta da suka amshi shawarar ya karu da kaso 20.4% duk da kalubalolin da aka fuskanta a duniya, baya ga jerin shirye-shiryen da aka yi nasarar cimmawa, ciki har da kammala gine-ginen cibiyar kasuwanci a sabuwar fadar mulkin kasar Masar dake kusa da birnin Alkahira, da fara gwajin zirga-zirgar layin dogo na zamani na farko na kasashen kungiyar ASEAN, da fara aiki da gadar Peljesac a kasar Croatia da ma tashar samar da wutar lantarki ta Karot a kasar Pakistan da dai makamantansu. Ban da wannan, a shekarar, karin wasu kasashe biyar sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa tare da kasar Sin bisa shawarar ziri daya da hanya daya.

Bana ne ake cika shekaru 10 da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar ziri daya da hanya daya. A cikin wadannan shekaru 10 da suka wuce, kasashen da suka amshi shawarar sai karuwa suke ta yi, wadanda suka yi ta inganta hadin gwiwarsu, kuma shawarar na ta kara samun karbuwa daga kasa da kasa. Shawarar da aka aiwatar ta samar da gadoji da tashoshin ruwa da hanyoyi marasa lisaftuwa a kasashen da suka karbi shawarar, wadanda suka kyautata rayuwar miliyoyin al’ummar kasashen, lamarin da ya shaida karfin hadin gwiwar kasa da kasa.

A wani sabon mafari, kasar Sin na sa ran aiwatar da shawarar tare da kasashen duniya cikin karin wasu shekaru 10 masu zuwa, ta yadda shawarar za ta haifar da karin alfanu ga kasashen duniya da al’ummominsu.(Lubabatu)

 

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
Daga Birnin Sin

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
Daga Birnin Sin

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Next Post
Muna Ta Tabka Abun Kunya Kan Rashin Sadio Mane A Cikinmu— Liverpool

Muna Ta Tabka Abun Kunya Kan Rashin Sadio Mane A Cikinmu— Liverpool

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.