• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ziri Daya Da Hanya Daya” Da Ke Haifar Da Alfanu Ga Al’ummar Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Al'ummar duniya

A kwanakin baya ne, aka kammala kashi na farko na layin dogo mai amfani da lantarki a jihar Lagos, tarayyar Nijeriya, wanda ke zama irinta ta farko a yammacin Afirka, haka kuma karin nasara da aka cimma a kokarin aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, ko kuma “Belt and Road Initiative” a Turance. Da yake kaddamar da aikin, gwamnan jihar Lagos Babajide Olusola Sanwo-Olu, ya bayyana shi a matsayin wanda zai saukaka matsalar zirga-zirga da ake fuskanta a jihar, kana abin koyi ga Nijeriya da ma sauran kasashen yammacin Afirka wajen shimfida layukan dogo.

A cikin shekarar da ta gabata, an aiwatar da hadin gwiwar “ziri daya da hanya daya” tare da dimbin nasarori, inda a cikin watanni 11 na farkon shekarar, jimillar kudin ciniki a tsakanin kasar Sin da sauran abokananta da suka amshi shawarar ya karu da kaso 20.4% duk da kalubalolin da aka fuskanta a duniya, baya ga jerin shirye-shiryen da aka yi nasarar cimmawa, ciki har da kammala gine-ginen cibiyar kasuwanci a sabuwar fadar mulkin kasar Masar dake kusa da birnin Alkahira, da fara gwajin zirga-zirgar layin dogo na zamani na farko na kasashen kungiyar ASEAN, da fara aiki da gadar Peljesac a kasar Croatia da ma tashar samar da wutar lantarki ta Karot a kasar Pakistan da dai makamantansu. Ban da wannan, a shekarar, karin wasu kasashe biyar sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa tare da kasar Sin bisa shawarar ziri daya da hanya daya.

Bana ne ake cika shekaru 10 da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar ziri daya da hanya daya. A cikin wadannan shekaru 10 da suka wuce, kasashen da suka amshi shawarar sai karuwa suke ta yi, wadanda suka yi ta inganta hadin gwiwarsu, kuma shawarar na ta kara samun karbuwa daga kasa da kasa. Shawarar da aka aiwatar ta samar da gadoji da tashoshin ruwa da hanyoyi marasa lisaftuwa a kasashen da suka karbi shawarar, wadanda suka kyautata rayuwar miliyoyin al’ummar kasashen, lamarin da ya shaida karfin hadin gwiwar kasa da kasa.

A wani sabon mafari, kasar Sin na sa ran aiwatar da shawarar tare da kasashen duniya cikin karin wasu shekaru 10 masu zuwa, ta yadda shawarar za ta haifar da karin alfanu ga kasashen duniya da al’ummominsu.(Lubabatu)

 

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
Next Post
Muna Ta Tabka Abun Kunya Kan Rashin Sadio Mane A Cikinmu— Liverpool

Muna Ta Tabka Abun Kunya Kan Rashin Sadio Mane A Cikinmu— Liverpool

LABARAI MASU NASABA

Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

Wani Sabon Hari Kan Al’ummar Da Ke Iyaka Da Katsina A Kano Ya Rutsa Da Mata 5

November 10, 2025
Matatun mai

Yadda Sojoji Suka Tarwatsa Haramtattun Matatun Mai 14 A Yankin Neja Delta 

November 10, 2025
Jibrin Kofa

Ɗan Majalisar Wakilai, Jibrin Ƙofa Ya Sauya Sheƙa Daga NNPP Zuwa APC

November 10, 2025
Boko haram

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.