ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

“Ziri Daya Da Hanya Daya” Da Ke Haifar Da Alfanu Ga Al’ummar Duniya

by CMG Hausa
4 years ago
Al'ummar duniya

A kwanakin baya ne, aka kammala kashi na farko na layin dogo mai amfani da lantarki a jihar Lagos, tarayyar Nijeriya, wanda ke zama irinta ta farko a yammacin Afirka, haka kuma karin nasara da aka cimma a kokarin aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, ko kuma “Belt and Road Initiative” a Turance. Da yake kaddamar da aikin, gwamnan jihar Lagos Babajide Olusola Sanwo-Olu, ya bayyana shi a matsayin wanda zai saukaka matsalar zirga-zirga da ake fuskanta a jihar, kana abin koyi ga Nijeriya da ma sauran kasashen yammacin Afirka wajen shimfida layukan dogo.

A cikin shekarar da ta gabata, an aiwatar da hadin gwiwar “ziri daya da hanya daya” tare da dimbin nasarori, inda a cikin watanni 11 na farkon shekarar, jimillar kudin ciniki a tsakanin kasar Sin da sauran abokananta da suka amshi shawarar ya karu da kaso 20.4% duk da kalubalolin da aka fuskanta a duniya, baya ga jerin shirye-shiryen da aka yi nasarar cimmawa, ciki har da kammala gine-ginen cibiyar kasuwanci a sabuwar fadar mulkin kasar Masar dake kusa da birnin Alkahira, da fara gwajin zirga-zirgar layin dogo na zamani na farko na kasashen kungiyar ASEAN, da fara aiki da gadar Peljesac a kasar Croatia da ma tashar samar da wutar lantarki ta Karot a kasar Pakistan da dai makamantansu. Ban da wannan, a shekarar, karin wasu kasashe biyar sun daddale yarjejeniyoyin hadin gwiwa tare da kasar Sin bisa shawarar ziri daya da hanya daya.

Bana ne ake cika shekaru 10 da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar ziri daya da hanya daya. A cikin wadannan shekaru 10 da suka wuce, kasashen da suka amshi shawarar sai karuwa suke ta yi, wadanda suka yi ta inganta hadin gwiwarsu, kuma shawarar na ta kara samun karbuwa daga kasa da kasa. Shawarar da aka aiwatar ta samar da gadoji da tashoshin ruwa da hanyoyi marasa lisaftuwa a kasashen da suka karbi shawarar, wadanda suka kyautata rayuwar miliyoyin al’ummar kasashen, lamarin da ya shaida karfin hadin gwiwar kasa da kasa.

ADVERTISEMENT

A wani sabon mafari, kasar Sin na sa ran aiwatar da shawarar tare da kasashen duniya cikin karin wasu shekaru 10 masu zuwa, ta yadda shawarar za ta haifar da karin alfanu ga kasashen duniya da al’ummominsu.(Lubabatu)

 

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

 

Al'ummar duniya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela
Daga Birnin Sin

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
Daga Birnin Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Next Post
Muna Ta Tabka Abun Kunya Kan Rashin Sadio Mane A Cikinmu— Liverpool

Muna Ta Tabka Abun Kunya Kan Rashin Sadio Mane A Cikinmu— Liverpool

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.