• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa al’ada, a farkon kowacce sabuwar shekara, ministan harkokin wajen kasar Sin kan ziyarci wasu kasashe a nahiyar Afrika. Kuma a bana ma hakan ce ta kasance, inda sabon ministan harkokin wajen Sin Qin Gang, ya fara ziyararsa a kasashen Afrika daga jiya Litinin, wadda kuma ita ce ziyararsa ta farko a ketare bayan dare kujerar.

Dangantakar kasar Sin da Afrika ba sabon abu ba ne, la’akari da cewa, wannan al’ada ta ziyarar ministan harkokin wajen Sin a nahiyar Afrika a duk farkon shekara, ta shafe shekaru 33 a jere ana gudanar da ita ba fashi. Wannan ya tabbatar da kasar Sin a matsayin jajirtacciya, mai cika alkwarinta, duk wuya duk rintsi. Haka zalika, ya nuna yadda Sin take daukar kasashen Afrika da muhimmanci, sabanin wasu kasashen dake daukar nahiyar a matsayin wurin yi wa babakere ko ci da gumin al’umma ko kuma neman cikar wasu burikansu na siyasa.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Kwarin Gwiwa Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya

Ba shakka, karfin alakar kasar Sin da Afrika ta zarce tunanin mutum, shi ya sa ma masu yada jita-jita da neman danniya da adawa da Sin, ke neman shafa mata bakin fenti domin shiga tsakaninta da kasashen Afrika. Sai dai, abun da ya kamata a fahimta shi ne, da kasar Sin tana da wata mummunar manufa dangane da alakarta da kasashen nahiyar da an gani a fili zuwa yanzu, kamar yadda aka ga dimbin ayyukan more rayuwa da ta yi, kuma take ci gaba da yi a kasashen.

Albarkacin kasar Sin, kasashen Afrika sun samu ci gaban tattalin arziki da zaman takewa da ingantuwar tsaro da fasahohi da kwarewa da kuma muhimman ababen more rayuwa da ba su samu ba daga iyayen gidansu masu mulkin mallaka.

Har ila yau, a wannan lokaci da ziyarar na ministan Sin din ya zo a daidai lokacin da kasar take saukaka matakanta na yaki da annobar COVID-19 da na shige da fice har ma da kyautata bangarorin zuba jarin waje, wata dama ce ga kasashen nahiyar na farfado da harkokinsu na kasuwanci da kasar Sin da fadada hadin gwiwa a bangarori daban-daban, domin wannan dama ce ’yan kasuwar Afrika suka dade suna jira, wanda zai taimaka wajen karfafa tattalin arzikinsu da rage tashin farashin kayayyaki da suke fama da shi.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu Wanda Ya Isa Ya Alakanta Ni Da Satar Dukiyar Jama’a – Buhari

Next Post

Masu Zuba Jari Na Kasashen Waje Na Da Kwarin Gwiwar Zuba Jari a Sin

Related

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

1 hour ago
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

2 hours ago
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

3 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

4 hours ago
Sin
Daga Birnin Sin

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

5 hours ago
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000
Daga Birnin Sin

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

6 hours ago
Next Post
Masu Zuba Jari Na Kasashen Waje Na Da Kwarin Gwiwar Zuba Jari a Sin

Masu Zuba Jari Na Kasashen Waje Na Da Kwarin Gwiwar Zuba Jari a Sin

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Sin

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.