ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Ministan Harkokin Wajen Sin: Sabuwar Dama Ce Ga Kasashen Afrika Na Farfado Da Tattalin Arzikinsu

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Bisa al’ada, a farkon kowacce sabuwar shekara, ministan harkokin wajen kasar Sin kan ziyarci wasu kasashe a nahiyar Afrika. Kuma a bana ma hakan ce ta kasance, inda sabon ministan harkokin wajen Sin Qin Gang, ya fara ziyararsa a kasashen Afrika daga jiya Litinin, wadda kuma ita ce ziyararsa ta farko a ketare bayan dare kujerar.

Dangantakar kasar Sin da Afrika ba sabon abu ba ne, la’akari da cewa, wannan al’ada ta ziyarar ministan harkokin wajen Sin a nahiyar Afrika a duk farkon shekara, ta shafe shekaru 33 a jere ana gudanar da ita ba fashi. Wannan ya tabbatar da kasar Sin a matsayin jajirtacciya, mai cika alkwarinta, duk wuya duk rintsi. Haka zalika, ya nuna yadda Sin take daukar kasashen Afrika da muhimmanci, sabanin wasu kasashen dake daukar nahiyar a matsayin wurin yi wa babakere ko ci da gumin al’umma ko kuma neman cikar wasu burikansu na siyasa.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Kwarin Gwiwa Ga Bunkasuwar Tattalin Arzikin Duniya

Ba shakka, karfin alakar kasar Sin da Afrika ta zarce tunanin mutum, shi ya sa ma masu yada jita-jita da neman danniya da adawa da Sin, ke neman shafa mata bakin fenti domin shiga tsakaninta da kasashen Afrika. Sai dai, abun da ya kamata a fahimta shi ne, da kasar Sin tana da wata mummunar manufa dangane da alakarta da kasashen nahiyar da an gani a fili zuwa yanzu, kamar yadda aka ga dimbin ayyukan more rayuwa da ta yi, kuma take ci gaba da yi a kasashen.

ADVERTISEMENT

Albarkacin kasar Sin, kasashen Afrika sun samu ci gaban tattalin arziki da zaman takewa da ingantuwar tsaro da fasahohi da kwarewa da kuma muhimman ababen more rayuwa da ba su samu ba daga iyayen gidansu masu mulkin mallaka.

Har ila yau, a wannan lokaci da ziyarar na ministan Sin din ya zo a daidai lokacin da kasar take saukaka matakanta na yaki da annobar COVID-19 da na shige da fice har ma da kyautata bangarorin zuba jarin waje, wata dama ce ga kasashen nahiyar na farfado da harkokinsu na kasuwanci da kasar Sin da fadada hadin gwiwa a bangarori daban-daban, domin wannan dama ce ’yan kasuwar Afrika suka dade suna jira, wanda zai taimaka wajen karfafa tattalin arzikinsu da rage tashin farashin kayayyaki da suke fama da shi.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Masu Zuba Jari Na Kasashen Waje Na Da Kwarin Gwiwar Zuba Jari a Sin

Masu Zuba Jari Na Kasashen Waje Na Da Kwarin Gwiwar Zuba Jari a Sin

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.