• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zulum Ya Bai Wa Matasan Biu 1,000 Tallafin Miliyan 100 Don Yin Jari

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Zulum Ya Bai Wa Matasan Biu 1,000 Tallafin Miliyan 100 Don Yin Jari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Babagana Zulum na Jihar Borno, ya ce ya bai wa matasa marasa aikin yi 1,000 tallafin Naira miliyan 100 a garin Biu.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga gwamnan kan harkokin yada labarai, Baba-Sheik Haruna, ya sanyawa hannu kuma ya fitar a Abuja ranar Juma’a.

  • Kotu Ta Soke Takarar Dare A Matsayin Wanda Zai Yi Wa PDP Takarar Gwamna A Zamfara
  • Tagomashin Da CBN Ya Samar Wajen Bunkasa Kanana Da Matsakaitan Sana’o’i

Ya ce tallafin, wanda aka gudanar a Kadafur da ke garin Biu, za a yi amfani da shi ne a matsayin jarin fara kasuwanci ga masu kananan sana’o’i domin bunkasa tattalin arzikin yankin.

Taron dai wani bangare ne na rangadin kwanaki uku da gwamnan ya kai hedikwatar Sanatan Borno ta Kudu, domin kaddamar da ayyuka daban-daban da gwamnatinsa ta aiwatar.

A yayin da yake kira ga wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da wannan tallafin da idon basira, gwamnan ya ce gwamnati za ta ci gaba da kokarin rage zaman kashe wando da yaki da fatara ta hanyar taimaka wa marasa galihu da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Ya bayyana cewa talauci, rashin aikin yi da rashin ilimi ne suka taka muhimmiyar rawa wajen bullar Boko Haram a jihar.

A tsawon wannan lokaci, Zulum ya kaddamar da Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Mega da ke Buratai mai daukar dalibai 1,500, sannan ya bude babbar makarantar Islamiyya ga dalibai 1,200 da ke Biu da kuma Sashen Sa ido da tantance Ilimi na Shiyya a garin Biu.

Tun da farko kwamishinan matasa, ci gaban wasanni da yaki da fatara, Saina Buba, ya ce an zabo wadanda suka amfana su 1,000 ne daga gundumomi a fadin karamar hukumar Biu.

Ya ce gwamnan, wanda tun a shekarar 2019, ya kaddamar da wasu tsare-tsare na tattalin arziki da ke bayar da tallafin kudi ga kanana da matsakaitan ‘yan kasuwa, bai bar masu nakasa da kuma tsofaffi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BiuBoko HaramBornoGwamnaMatasaTalauciTallafiYaki Da FataraZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Soke Takarar Dare A Matsayin Wanda Zai Yi Wa PDP Takarar Gwamna A Zamfara

Next Post

Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

Related

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

7 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

10 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

15 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

16 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin GargaÉ—i Da Ta Fara

18 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

21 hours ago
Next Post
Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

Farfadowar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Zarce Yadda Ake Tsammani

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga KwaÉ—ayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga KwaÉ—ayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.