Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya mayar da iyalai 6,000 da suka rasa matsuguninsu saboda hare-haren Boko Haram zuwa garuruwansu na asali.
Yawancin mutanen sun fito ne daga ƙananan hukumomin Dikwa da Mafa.
- Aikin Hajjin 2025 Ya Fara A Hukumance Yayin Da Tawagar NAHCON Ta Musamman Ta Tashi Zuwa Makkah
- Jiragen Kasa Na Sin Sun Yi Jigilar Fasinjoji Sama Da Miliyan 100 A Lokacin Hutun Ranar Ma’Aikata
Gwamna Zulum ya yi wannan jawabi ne a ranar Litinin a sansanin ‘yan gudun hijira na Muna da ke Maiduguri, inda aƙalla iyalai 11,000 ke zaune saboda rikicin da ya daɗe yana faruwa a jihar.
Ya ce dole ne a mayar da mutane gidajensu saboda yawaitar aikata laifuka a cikin sansanin, ciki har da karuwanci, tada zaune tsaye, cin zarafin yara da sauran muggan laifuka.
“Boko Haram ba za ta ƙare ba sai an dawo da jama’a gida su fara rayuwa yadda ya kamata,” in ji Zulum.
“Mun rufe dukkan sansanonin ‘yan gudun hijira da ke cikin Maiduguri. Yanzu haka saura biyu da ba na hukuma ba. Mun riga mun dawo da kashi 75 na ‘yan sansanin Muna gida, saura kashi 25 za su koma cikin kwanaki masu zuwa.”
Kowane iyali sun samu tallafin abinci, kayan gini da kulawar lafiya.
Haka kuma, kowane magidanci mace ko namiji za a ba shi Naira 100,000, yayin da matan gidan za su ƙara samun Naira 50,000 don taimaka musu da buƙatunsu na yau da kullum.
Za a Ƙara Inganta Cibiyar Koyo Sana’o’i a Gidan Gyaran Hali
Tun da safiyar ranar Litinin, Gwamna Zulum ya kai ziyara gidan gyaran hali na manyan laifuka da ke Maiduguri.
Ya ce za a inganta cibiyar koyar da sana’o’i da ke gidan don taimaka wa fursunoni su koyi sana’a da za su yi amfani da ita bayan an sake su.
“Manufar ɗaure mutum a gidan gyaran hali ita ce gyara halayensa, ba wai tsare shi kawai ba. Wannan ba zai yiwu ba sai akwai kayan aikin koyarwa da ake buƙata” in ji Zulum.
“Za mu duba wasu daga cikin fursunonin da ke da ƙananan laifuka, mu gani ko akwai yiwuwar a sake su bisa doka.”
Zulum ya samu rakiyar ɗan Majalisar Tarayya, Bukar Talba, shugaban ma’aikatansa na riƙon ƙwarya, mai ba shi kan harkokin addini da wasu jami’an gwamnati.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp