• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴancin Ƙananan Hukumomi Zai Taimaka Wajen Magance Matsalolin Tsaro – COAS

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Tsaro
0
Ƴancin Ƙananan Hukumomi Zai Taimaka Wajen Magance Matsalolin Tsaro – COAS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Hafsan Sojin ƙasa (COAS), Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya tabbatar da cewa bayar da cikakken ‘yancin cin gashin kai ga ƙananan hukumomi zai taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalolin tsaro a Nijeriya. Da yake jawabi yayin bikin Sojojin Nijeriya a garin Jos na jihar Filato, Janar Lagbaja ya jaddada muhimmiyar rawar da ci gaban ƙasa ke takawa wajen magance matsalolin rashin tsaro.

Ya yi tambaya kan dalilin da ya sa masu faɗa a ji ke ƙin amince wa da cin gashin kan ƙananan hukumomi, wanda yawancin ‘yan ƙasar ke buƙata, ya kuma bayyana cewa ‘yancin cin gashin kan ƙananan hukumomi na da matuƙar muhimmanci wajen kawo ci gaba a matakin farko.

  • Rahoto Ya Bankado ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaron Nijeriya 200 Masu Kadarori A Dubai
  • Sin Na Fatan Amurka Za Ta Martaba Ikon Mulkin Kai Tsaro Da Moriyar Ci Gabanta

Ya yi nuni da cewa kafa kwamitoci ko ma’aikatun gwamnati kawai ba zai wadatar ba, ya kuma bayyana buƙatar samar da ingantaccen shugabanci a matakin ƙananan hukumomi domin daƙile matsalar rashin tsaro.

Janar Lagbaja ya yi nuni da taɓarɓarewar tsaro musamman a yankin Arewa maso Gabas, inda ya kwatanta sauƙin tafiye-tafiye a baya da matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu sakamakon rashin shugabanci na gari a matakin ƙananan hukumomi. Ya jaddada cewa wannan batu ya wuce yankin Arewa maso Gabas zuwa Arewa ta Tsakiya da sauran yankunan Nijeriya.

Duk da ƙin amincewa da cin gashin kan ƙananan hukumomi da gwamnonin jihohi suka yi a baya, gwamnatin tarayya na ci gaba da bin matakan bai wa ƙananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArmyLagbajaLocal governmentState GovernmentTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarakunan Da Ganduje Ya Nada Tamkar Kwamishinoni Ne – Shugaban NNPP

Next Post

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)

Related

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina

4 days ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

1 week ago
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

2 weeks ago
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
Tsaro

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

3 weeks ago
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

3 weeks ago
Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato
Tsaro

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

4 weeks ago
Next Post
ilimi

Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.