• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

by Leadership Hausa
1 year ago
in Adabi, Ilimi, Labarai
0
Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsofaffin daliban Sashen’ Koyar da Harsunan Nijeriya na Jami’ar Bayero ‘yan shekarar 2015 sun sabunta Dakin Karatu na Sashen tare da gyaran wasu sassa na Sashen a Jami’ar.

A ranar Alhamis 02 ga watan Mayun 2024 aka gudanar da kasaitaccen bikin bude Dakin Karatu na Marigayi Farfesa M.A.Z Sani da tsofaffin daliban Sashen suka sabunta shi bisa jagorancin shugaban daliban na 2015, Alhaji Hassan Baita Ubawaru, wanda ya samu wakilcin Sakataren Kungiyar daliban, Muhammad Bashir Amin.

Sakataren Kungiyar Dalibai 'Yan Ajin 2015, Muhammad Bashir Amin, yayin da yake yi wa Shugaban Jami'ar Bayero bayani yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
Sakataren Kungiyar Dalibai ‘Yan Ajin 2015, Muhammad Bashir Amin, yayin da yake yi wa Shugaban Jami’ar Bayero bayani yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
  • Za Mu Sabonta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita
  • Jami’ar Bayero Kano Za Ta Karrama Sanata Barau Da Adesina Da Digirin Girmamawa

A nasa jawabin Shugaban Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya na Jami’ar Bayero, Dr. Jibril Shu’aibu Adamu, ya yaba da kokarin daliban ya kuma sanarwa da Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, irin kokarin da daliban suke yi na tallafawa Sashen, inda ya ce ko a kwanan nan tsofaffin daliban sun bai wa Sashen sababbin injinan nadar bayanan takardu uku tare da gyaran wasu sassa na Sashen.

Shugaban Jami'ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas da Dr. Jibril S. Adamu da Alh. Baita Ubawaru yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
Shugaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas da Dr. Jibril S. Adamu da Alh. Baita Ubawaru yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani

A nasa jawabin, Shugaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya yaba da kokarin daliban da irin tallafin da suke bai wa Sashen, ya kuma yi alkawarin ci gaba da tallafawa Sashen daga bangaren shugabancin Jami’ar.

Sagir ya ce, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya shi ne Sashe daya rak da ya fi kowane Sashen hulda da kasashen waje da suka hada da kasar Sin da Holandiya da Jamus da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

A jawabin shugaban daliban, Alh. Hassan Baita Ubawaru, wanda ya samu wakilcin Sakataren kungiyar daliban, Muhammad Bashir Amin, ya ce, za su ci gaba da tallafawa Sashen ta bangarori da dama, tare da aiki kafada-kafada da juna don ganin an inganta harkokin koyo d koyarwa da bunkasa Harshe da Adabi da Al’adun Hausawa.

Alh. Baita Ubawaru yayin da yake jawabi a wurin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani a Jami'ar Bayero.
Alh. Baita Ubawaru yayin da yake jawabi a wurin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani a Jami’ar Bayero.

A nasa jawabin, Alh. Baita Ubawaru, wanda shi ne mahaifin shugaban daliban na 2015, kuma daya daga cikin wandanda suka tallafawa Shugaban Jami’ar wajen kaddamar da bude Dakin Karatun a yayin bikin, ya bayyana farin cikinsa tare da fatan Dakin Karatun ya zama mai amfanar da daliban Sashen da sauran al’umma baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUKDakin KaratuJami'ar Bayero
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fatima Mai Zogale: Baturiyar Da Allah Ya Yi A Dare Daya

Next Post

Shawara Ya Kamata Malamai Su Rika Bai Wa ‘Yan Kannywood Ba Zagi Ba – Daushe

Related

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
Tsaro

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

10 hours ago
Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano
Labarai

Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

12 hours ago
Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi
Labarai

Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

13 hours ago
Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
Manyan Labarai

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

18 hours ago
Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
Labarai

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

20 hours ago
Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
Labarai

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

20 hours ago
Next Post
Shawara Ya Kamata Malamai Su Rika Bai Wa ‘Yan Kannywood Ba Zagi Ba – Daushe

Shawara Ya Kamata Malamai Su Rika Bai Wa ‘Yan Kannywood Ba Zagi Ba - Daushe

LABARAI MASU NASABA

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

June 22, 2025
Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

June 22, 2025
Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

June 22, 2025
Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

June 22, 2025
Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.